Kazalika, a Arewacin Nijeriya, Robar Tumatir mai nauyin kilo 25  yanzu, ana sanar da ita kan Naira 6,500.

Shugabar kungiyar masu noman Tumatair da sarrafa shi ta kasa, Rabiu Zuntu ta sanar da cewa, an samu girbin Tumatir mai yawan gaske, duba da cewa; yanzu ana cikin watan Fabrairu, lokacin da ake samun yawaitarsa.

A cewar tata, tarin yawan nasa ne ya sa aka samu faduwar farashinsa a kasuwanni, wannan dalili ne ma ya sanya, don gudun kada manoman su yi asara; suke sayar da shi kan farashi mai sauki.

“Daga watannin Janairu, Fabrairu zuwa Maris; ana samun kwantan Tumatir, yanzu kuma muna da injinoni masu kyau na sarrafa Tumatirin, wanda hakan zai sa a samu raguwar farashin”, in ji Zuntu.

Har ila yau, Zuntu ta yi kira ga ‘yan Nijeriya da su yi amfani da wannan dama, domin sayen Tumatirn da yawa, kafin daga nan zuwa watan Afrilu.

“Akasari mukan bai wa masu amfani da kayan amfanin gona shawarar cewa, su sayi Tumatirin da dama a irin wannan lokaci, don adana shi”, a cewar ta Zuntu.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [17]

Misalan Wannan Hassada:
1. Hassadar Fir’auna a Kan Annabi Musa (AS):
Fir’auna ba ya son aiken da Allah Ya yi wa Annabi Musa (AS) ba, domin yana tsoron cewa mulkinsa zai ƙare. Ya so cewa wannan matsayi na shugabanci da iko ya kasance a gare shi kawai.

Allah Ta’ala Ya ce:” Fir’auna kuma ya ce: ‘Ku bar ni in kashe Musa, kuma ya je ya kira Ubangijinsa! Lallai ni ina tsoron ya canza addininku, ko kuma ya bayyana ɓarna a cikin ƙasa.'” Suratu Gãfir aya ta 26.

Fir’auna bai so wani ya sami iko ko shugabanci sai shi, don haka ya so ya kashe annabi Musa (AS) domin mulkinsa ya dore.

2. Hassadar Ƙuraishawa ga Annabi Muhammad (SAW):
A lokacin da Manzon Allah (SAW) ya bayyana da’awarsa, manyan shugabannin Ƙuraishawa sun ji haushin hakan, domin suna son a ce su ne kawai suka mallaki wannan matsayi na shugabanci da daraja. Allah Ta’ala Yana cewa “ Yanzu su ne suke raba rahamar Ubangijinka (ta annabi)? Mu ne muka raba musu arziƙinsu a rayuwar duniya. Mu muka ɗaukaka darjojin sashinsu a kan sashi, don wani sashi ya riƙi wani sashi mai yi masa hidima. Rahamar Ubangijinka kuma ita ta fi abin da suke tarawa na duniya.” Suratuz-Zukhruf aya ta 32.

Illolin Wannan Hassada:
Rashin Yarda da Ƙaddarar Allah: Mutum mai irin wannan hassada yana ƙin yarda Allah Ya raba ni’imomi. Yana jin cewa shi ya fi cancanta da wata ni’ima fiye da wanda yake da ita. Wannan yana nuni da ƙarancin imani.

Haddasa Gaba da Rikici: Wannan nau’in hassada yana jawo matsaloli a cikin zamantakewa. Idan mutum yana da burin hana wasu cin gajiyar ni’imar da Allah Ya ba su, to hakan yana haifar da gaba, kishi, da yaƙe-yaƙe a cikin al’umma.

Rashin Albarka a Rayuwa: Allah Ba ya albarkantar da wanda yake da zuciyar hassada. Mutumin da yake son ya hana wani alheri don shi ya mallake shi, sau da yawa ba zai kai ga hakan ba, kuma ko da ya samu, ba zai sami albarka a ciki ba.

Ruɗewa da Rashin Hankali: Mai irin wannan hassadar baya samun kwanciyar hankali. Yana jin kishi da tsananin damuwa idan wani yana cikin ni’ima. Wannan yana iya haifar da ciwon zuciya, matsanancin damuwa, da rashin kwanciyar hankali da nutsuwa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • SDP: Ba Mu Yi Wa Kowa Alƙawarin Takarar Shugaban Ƙasa Ba
  • Mutum 2,000 za su riƙa kamuwa da cutar HIV duk rana a duniya — MDD
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [17]
  • Ɗansanda Ya Kashe Matar Abokin Aikinsa, Ya Jikata Wasu Biyu A Ribas
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [16]
  • Yadda garin Zip ya nutse a Kogin Binuwai
  • Mata sun ƙwace kasuwancin kayan lambu a Gombe
  • Kao Kim Hourn: Ba Ta Hanyar ‘Siddabaru’ Kasar Sin Ta Cimma Nasarori A Fannin Ci Gaba Ba Sai Dai Ta Hanyar Aiki Tukuru Kuma Mai Dorewa
  • Hikimar Gwamnatin Jihar Jigawa Na Kaddamar Da Shirin Gina Rijiyoyin Burtsatsan Noman Rani
  •  “Yan Ta’adda Sun Kai Hari Akan Masu Salla A Jamhuriyar Nijar