Gidauniyar ‘TY Buratai Literary Initiative (TYBLI)’ ta kaddamar da shirye-shiryen tallafinta na 2025 wanda ta kudiri aniyar bunkasa ilimi da tsarin koyo a tsakanin daliban Nijeriya. Shirin wanda gidauniyar Laftanar Janar Tukur Yusuf Buratai (mai ritaya) ta kirkiro kuma ta dauki nauyin wannan shiri na da nufin kwadaitar da koyon Adabin rubutu da kuma bai wa daliban da suka fi hazaka tukuici a fadin kasar nan.

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kashe Naira Tiriliyan 4.2 Don Aikin Manyan Hanyoyi Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kashe Naira Tiriliyan 4.2 Don Aikin Manyan Hanyoyi Da take jawabi a wani taron manema labarai, Dokta Lizi Ben-Theanacho, shugabar Gidauniyar ta TYBLI, ta jaddada kudirin Gidauniyar na bunkasa adabin rubutu ta hanyar samar da littattafai da kyaututtuka ga dalibai masu hazaka. “Abu na farko da muke fatan aiwatarwa shi ne, mu ba da gudummawa don samar da ilimi mai zurfi a Nijeriya ta hanyar samar da littattafai, tabbatar da ingancin kayan karatun da suka dace. Daga nan, sai mu zakulo dalibai masu hazaka, mu gwangwaje su da kyaututtuka na ban mamaki. “TYBLI Gidauniya ce ta wayar da kan jama’a da bayar da tallafi ga al’umma wacce Laftanar Janar TY Buratai (mai ritaya) ya kirkiro kuma ya dauki nauyin aiwatarwa.” in ji ta.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Brice Ologui Ya Lashe Zaben Shugaban Kasar Gaban Da Kashi 90.35% A Jiya Lahadi

Shugaban gwamnatin rikon kwarya na kasar Gabon wanda kuma ya jagoranci juyin mulkin da aka yiwa Ali Bongo tsahon shugaban kasar ya lashe zaben da aka gudanar a jiya Lahadi tsakanin yan takara 7 har da shi.

Shafin yanar gizo na labarai ‘Africa News” ya bayyana cewa Oligui dan shekara 50 a duniya, shi ne babban dogarin sojoji masu tsare fadar shugaban kasar Gaban, a lokacinda ya jagoranci juyin mulkin da ya kawo karshen mulkin da yan gidan Bogo suka yi na shekaru kimani 50 a kasar.

Labarin ya kara da cewa kashi 2/3 na mutanen Gabon wadanda yawansu bai fi miliyon 2.3 ba suna cikin talauci a cikin kasa wacce take da arziki mai yawa.

Brice zai jagoranci kasar na tsawon shekaru 7 masu zuwa kuma yana iya sake shi takarar shugabancin kasa karo na biyu.

Yan takara 6 ne suka tsaya tare da Brice amma mai binsa bai sami fiye da kashi  3 % na kuri’un da aka kada ba sannan yawan fitowar mutane masu zabe ya kai kashi 70.4% wanda ya nuna cewa an sami sauyi babban a cikin harkokin siyasar kasar ta Gabaon.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Samarwa Matasa Abun Yi Shi Zai Kawo Ƙarshen Ta’addancin Boko Haram Da ‘Yan Bindiga – Zulum 
  • Hajj 2025: Hukumar Alhazai Ta Shirya Taron Bita Ga Mahajjata a Jihar Kwara
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bukaci Jami’an Tsaro Mata Su Rika Sanya Hijabi Yayin Aiki
  • Majalisar Kaduna ta Amince da Kudirin Kula da Lafiyar Kwakwalwa na Jihar
  • Duk da samun koma baya: Najeriya ce kasa mafi arzikin danyen mai a Afirka —OPEC
  • Noman rake: Najeriya da China sun kulla yarjejeniyar kasuwancin $1bn
  • Rundunar “Gulani” Ta Shiga Sahun Masu Kin Amincewa Da Yaki
  • Iran, Iraki Sun Karfafa Dangantakar Makamashi
  • Brice Ologui Ya Lashe Zaben Shugaban Kasar Gaban Da Kashi 90.35% A Jiya Lahadi
  • Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa