Kasar Sin ta yi watsi tare da nuna kin amincewarta da tsegumin da aka yi mata daga bangaren Amurka, inda sakataren harkokin wajen Amurkar, Marco Rubio ya yi wasu zarge-zarge marasa tushe balle makama a kan kasar ta Sin, yayin da yake ziyara a yankin Latin Amurka da Caribbean.

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana hakan a yau Juma’a, inda ya kara da cewa, kalaman marasa tushe daga bangaren Amurka, wadanda suka karkata zuwa tunanin yakin cacar-baka da nuna son zuciya, zarge-zarge ne kawai na yamadidi a kan kasar Sin da aka kitsa da nufin haifar da sabani tsakaninta da kasashen da abin ya shafa na Latin Amurka da Caribbean, wanda kuma hakan tsoma baki ne a harkokin cikin gidan kasar Sin, da kuma gurgunta hakkoki da moriyar kasar Sin ta halaliya da kuma muradunta.

Game da hadin gwiwar dake tsakanin Sin da yankin na LAC kuwa, mai magana da yawun ma’aikatar ya ce, kasar Sin ta kuduri aniyar karfafa abokantaka da hadin gwiwa tare da kasashen na LAC bisa tsarin mutunta juna, da daidaito, da cin moriyar juna, da bude kofa, da hada kai, da sauran harkokin hadin gwiwar samun nasara ga ko wane bangare. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ban taɓa fuskantar tsangwama a Kannywood ba — Prince Aboki

Daraktan Fim ɗin Mai martaba, Prince Daniel (ABOKI), ya ce ba gaskiya ba ne batun da ake yaɗawa cewa yana fuskantar tsangwama a Kannywwod saboda bambancin addininsa.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, Aboki ya ce shi ma batun cewa ana nuna masa bambamci a Nollywood saboda ɗan arewa ne ba shi da tushe balle makama.

Ribas: Za mu ɗauki matakan da za su shafi tattalin arzikin Nijeriya — ’Yan ƙwadago Ban sani ba ko zan tsaya takara a 2027 — Atiku

“Wasu labarai da aka wallafa na nuna cewa wai masana’antar Kannywood ta ƙi amincewa da ni saboda addini na, ita kuma Nollywood saboda ni ɗan Arewa ne.

“Da farko dai ban yi hira da wata jarida ko kafar yaɗa labarai ba dangane da wannan batu. Amma duk da haka bari na ɗan yi ƙarin haske.

“Na halarci wani taron masana’antar Nollywood da Hollywood a birnin Los Angeles na Jihar California da ke Amurka a farkon wannan watan, inda a sashen tambaya da amsa na taron aka tambaye ni ƙalubalen da muka fuskanta lokacin fim ɗin Mai Martaba da gwagwarmayar da muka yi kafin kai wa matakin kambun fina-finan duniya na Oscar.

“Na faɗi abubuwa da dama da suka haɗa da fargabar matsalar tsaro da na masu ɗaukar nauyi kasancewar babu wanda yake son yin kasadar ba mu kuɗinsa, la’akari da cewa ni sabon darakta ne wanda ke aiki tare da sababbin jarumai.

“A wani lokacin ɓangaren masana’antar Kannywood na yi mana kallon ‘yan Nollywood, su ma Nollywood suna kallonmu a matsayin ‘yan Kannywood, saboda kawai ni ɗan Arewa ne.

“Na yi wannan bayanin ne da kyakkyawar niyya domin taimaka wa masu sauraro a cikin zauren su fahimci ɓangarorin masana’antar Fina-finai a Najeriya da kuma yadda yake da ƙalubale a gare mu a lokacin.

“Domin fayyace zahiri, masana’antar Kannywood ba ta taɓa nuna min ƙiyayya ba ta ƙabilanci ko addini.

“Hasalima, masana’antar ce babban ginshiƙin goyon bayan da na samu a matsayina na mai shirya fim.

“An nuna min ƙauna a fili ta hanyar babban goyon bayan da muka samu daga masu kallo da sauran al-umma a lokacin da muka nuna fina-finanmu a gidajen kallo, da kuma ƙarfafawa daga ƙwararrun ‘yan masana’antar tsofaffi da sababbin shiga,” in ji shi.

Fim ɗin Mai martaba dai an haska shi ne kimanin watanni takwas da suka gabata, kuma ci gaba ne kan wasan kwaikwayon gidan Rediyon Arewa da ke Kano mai taken ‘Kasar Jallaba”, inda Prince aboki ke aiki a matsayin jagoran sashin shirye-shirye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ban taɓa fuskantar tsangwama a Kannywood ba — Prince Aboki
  • Araqchi: Har yanzu Iran ba ta mayar da amsa ga wasikar Trump kan tattaunawar nukiliya ba
  • Kasuwar Kayayyakin Masarufi Ta Sin Za Ta Ci Gaba Da Nuna Yanayin Bunkasa Bisa Daidaito A Bana
  • Alamar Deepseek” Ta Bude Kofar Gyara Na Kara Kunno Kai A Harkokin Duniya
  • Iran Ta Turkiyya Sun Bukaci kasashen Musulmi Su Magance matsalar Jinkai A Kasar Palasdinu Da Aka Mamaye
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Zargin Kasar Amurkan Dangane Da Kamfanonin Man Fetur Na Kasar Ba Gaskiya Bane
  • An Yi Taron Tattaunawar Kasa Da Kasa Kan Damammakin Da Sin Ke Gabatarwa A Rasha
  •  Arakci: Babu Wanda Zai Yi Tunanin Kawo Wa Iran Hari
  • Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Sanata Steve Daines
  • Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya