HausaTv:
2025-03-25@20:00:03 GMT

Kudin Ajiyar Najeriya Na Kasashen Waje Sun Ragu Da Dalar Amurka Biliya 1.79

Published: 7th, February 2025 GMT

Bayanin da babban bankin kasar ta Najeriya ya fitar, ya bayyana cewa an sami wannan koma bayan ne a cikin makwanni uku da su ka gabata.

Bayanin na babban bankin na Najeriya ya ci gaba da cewa, kudaden ajiyar Najeriya na waje da a cikin watan Disamba sun kai dala biliya 40,887, sun ragu, sun zama dala biliyan $39.

723 daga ranar 31 ga watan Janairu 2025.

An bayyana koma bayan ne a kudaden waje na ajiya da babban bankin kasar yake da su, da ya kamata ace a ranar 4 ga watan Febrairu ne za a fitar da kididdiga akan halin da kudaden wajen suke ciki,amma ba a yi ba.

Bugu da kari  wannanbayanin  ya fito ne daga kamfanin dake kula da  kai da komawar kudaden Waje  Bismack Rewane da yake hasashen samun raguwar kudaden ajiyar na Najeriya a tsakanin shekarar 2025-2026 sai sami koma baya da kaso 11.47,wato zuwa dala biliyan 36.21, yayin a a cikin shekarar 2026 zai zama dala biliyan 37.65,alhali a 2024 ya kasance dala biliyan 40.9.

Farashin Naira idan aka kwatanta ta da Dala, a  3 ga watan nan  na Febrairu shi ne ; Naira 1,500.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: dala biliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Kusa A Kungiyar Hamas Salah Al-Bardawil Ya Yi Shahada

Kungiyar gwagwarmayar Falastinawa ta Hamas ta fitar da wata sanarwa dangane da shahadar Salah al-Bardawil, mamba a ofishin siyasa na kungiyar kuma wakilin majalisar dokokin Falasdinu.

A rahoton tashar Al-Alam, bayanin Hamas yana cewa: Dr. Salah Al-Bardawil, wanda ya yi fice a fagen siyasa, kafofin watsa labarai, da fagage na kasa da kasa, kuma ake kallonsa a matsayin daya daga cikin manyan kusoshin Hamas, wanda yake a kan gaba wajen gwagwarmaya da  sadaukarwa, ya yi shahada a kan tafarkin gaskiya.

Bayanin ya ci gaba da cewa: Bai taba gazawa wajen gudanar da ayyukansa na jihadi da hidima ga al’ummar Palastinu ba, ya kuma ci gaba da yin gwagwarmaya kan turba ta gaskiya da neman ‘yanci har zuwa karshen rayuwarsa.

Hamas ta jaddada cewa,  jinin Dakta Al-Bardawil da matarsa ​​da sauran shahidai wata fitila ce da za ta haskaka hanyar samun ‘yanci ga al’ummar Falastinu, kuma laifuffukan makiya ba za su taba raunana azama da jajircewar ‘yan gwagwarmaya a Falastinu ba.

A karshen wannan sanarwa da ta fitar a wannan Lahadi 23 ga Maris, 2025, kungiyar Hamas ta yi fatan samun rahama da aljannah ga Dr. Salah Bardawil da matarsa, tare da sauran wadanda suka yi shahada a kan tafarkin gaskiya.

Salah Al-Bardawil da matarsa ​​sun yi shahada ne a daren ranar 23 ga watan Ramadan, bayan wani hari da yahudawan sahyuniya suka kai a kan tantin su da suke a  yankin Al-Mawasi da ke yammacin birnin Khan Yunus.

Wannan harin dai wani bangare ne na kisan gilla da yahudawan Haramtacciyar Kasar Isra’ila  suke ci gaba da yi kan al’ummar Gaza marasa kariya, tare da samun cikakken goyon baya da karfin gwiwa da dukkanin taimako kan hakan daga gwamnatin kasar Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Turkiyya Sun Bukaci kasashen Musulmi Su Magance matsalar Jinkai A Kasar Palasdinu Da Aka Mamaye
  • An Ɗauko Sojoji Daga Waje Don Horas Da Dakarun Nijeriya 
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Ake Yi Wa ‘Yan Majalisar Ƙasa Kiranye
  • Sin Ta Sanar Da Dokar Dakile Takunkuman Kasashen Waje
  • Babban Kusa A Kungiyar Hamas Salah Al-Bardawil Ya Yi Shahada
  • NAJERIYA A YAU: Yadda watan Ramadana ke tasiri a harkokin kasuwanci
  • Masanin Amurka: Matakan Kariyar Cinikayya Da Amurka Ke Aiwatarwa Babban Kuskure Ne
  • Jakadan Sin A Amurka: Mayar Da Karin Haraji Makami Kaikayi Ne Da Zai Koma Kan Mashekiya
  • Gombe Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.1 Don Samar Da Fitilun Hanya Masu Aiki Da Hasken Rana
  • Amurka ta cire tukuicin wanda ya bayar da bayani kan mataimakin shugaban Taliban