Aminiya:
2025-04-14@20:28:26 GMT

An kashe ɗan banga da yin garkuwa da ’yan mata 6 a Neja

Published: 7th, February 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da wasu ’yan mata shida masu shekaru tsakanin 15 zuwa 17 a yankin unguwar Pandogari da ke Ƙaramar hukumar Rafi ta Jihar Neja.

Mazauna garin sun shaida wa Aminiya cewa, da tsakar daren Laraba ne ’yan bindigar suka kaiwa unguwarsu hari inda suka kashe wani ɗan banga mai suna Aliyu Aminu tare da yin garkuwa da ’yan matan.

’Yan fashin teku sun sace jirgin fasinja mutum 11 sun ɓace a Ribas Jirgin Amurka ɗauke da mutum 10 ya ɓace

Mazauna yankin sun ce, maharan da suke da yawa sun shiga cikin unguwar ne daga yankin Birnin Gwari, ta Kwalejin fasaha ta Mamman Kontagora da ke Pandogari.

Majiyoyi sun ce an kai ’yan matan da aka sace zuwa dajin Kwangel.

Ɗaya daga cikin majiyar ta ce, ’yan bindigar sun shiga gida gida a lokacin da suka kai farmakin cikin dare.

“Harin da aka kai a daren Laraba shi ne na uku a cikin mako guda. Tun bayan sasantawa da gwamnatin Jihar Kaduna ta yi da su, sun yi ta kai mana hari. Tattaunawa da sasantawa da mazauna Birnin Gwari ba su amfanar da mu ba.

“Waɗannan hare-haren sun sake dawowa tun ranar da Jihar Kaduna ta sasanta da su a Birnin Gwari. A makon da ya gabata, sun zo sun yi garkuwa da mutane ciki har da mai unguwar. Sun zo sau biyu kafin daren Larabar,” in ji shi.

Shugaban Ƙaramar hukumar Rafi, Ayuba Usman Katako ya tabbatar da faruwar harin a cikin wani shirin Hausa mai suna Tsalle Ɗaya ta gidan rediyon Prestige FM, inda ya ce akwai buƙatar gwamnatocin Neja da Kaduna su haɗa kai don ganin an samu zaman lafiya a jihohin biyu.

“Gaskiya ne ’yan bindiga sun kai hari a unguwar Pandogari. Hasali ma, ba wannan ne kawai harin da aka kai a makonni biyun da suka gabata ba. Harin na Laraba shi ne na uku.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: dajin Kwangel Rafi

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya

Wani babban jami’in Diblomasiyya na kasar Iran ya bada sanarwan cewa zagaye na biyu a tattaunawa ba kai tsaye ba tsakanin JMI da Amurka za’a gudanar da shi ne a kasashen Turai a ranar 19 ga watan Afrilun wannan shekara ta 2025.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto mataimakin ministan harkokin waje na JMI kan al-amuran da suka shafi siysa Majid Takht-Ravabchi yana fadar haka a jiya Lahadi a lokacinda yake gabatarwa Majalisar dokokin kasar Iran rahoto kan taron tawagar Amurka da kuma JMI a birnin Mascat na kasar Omman a ranar Asabar da ta gabata.

Jami’in diblomasiyyar ya kara da cewa, a tattaunawar da ba kai tsaye ba tsakanin kasashen biyu a ranar Asabar da ta gabata yayin kokarin gano, wuri guda wanda zasu iya tsayawa a kansa don gina tattaunawar a kansa. Takht-Ravanchi ya nakalto tawagar gwamnatin Amurka na cewa da gaske suke a tattaunawar, kuma basa neman yaki da kasar Iran, banda haka a shirye suke su saurari korafe korafe gwamnatin JMI. A ranar Asabar da ta gabace ministan harkokin wajen kasar Amurka da wakilin kasar Amurka a harkokin gabas ta tsakiya Steve Witkoff suka gudanar da zagaye na farko a tsakanin kasashen biyu a birnin Mascat na kasar Omman. Tashar talabijin ta Al-Manar ta kasar Lebanon ta nakalto shafin yanar gizo na larabarai na Axion na fadar cewa taro nag aba zai kasance a birni Roma na kasar Italiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Ceto Fasinjoji 16 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Filato
  • ’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato
  • Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Amnesty Ta Zargi  Rundunar “RSF” Ta Sudan Da Cin Zarafin Mata
  • Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Gwaska da mayaƙa 100 a Katsina
  • MDD: Mafi Yawancin Wadanda Yaki Ya Ci A Gaza Mata Ne Da Kananan Yara
  • Yemen Ta Maida Martani Kan Wasu Cibiyoyin Ajiyar Makamai A Yaffa Don Tallafawa Gaza
  • Iyaye Mata Sun Bukaci A Rika Samar Da Kayayyakin Bada Tazarar Haihuwa Akan Lokaci