Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta sanar a yau Juma’a cewa, daga ranar 9 zuwa 12 ga wata, wakilin musamman na shugaba Xi Jinping, Zhang Guoqing zai tafi kasar Faransa domin halartar taron koli kan ayyukan fasahar kirkirarriyar basira ta AI, bisa gayyatar da mai karbar bakuncin taron ta yi masa.

Zhang mamba ne na ofishin siyasa na kwamitin koli na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kuma mai mukamin mataimakin firaminista a majalisar gudanarwar kasar Sin.

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lin Jian ya bayyana cewa, ta hanyar halartar taron, kasar Sin tana fatan karfafa cundayar juna da mu’amala da dukkan bangarori, da samar da daidaito kan hadin gwiwa, da kara matsa kaimi ga aiwatar da yarjejeniyar MDD kan fasahar zamani. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

 Aljeriya Ta Kori Jami’an Diflomasiyya Faransa 12

Gwamnatin kasar Ajeriya ta bayyana jami’an diflomasiyyar Faransa da suke kasar su 12 a matsayin ‘wadanda ba a bukatar ganinsu” a cikin kasar, tare da yin kira a gare su da su fice a cikin sa’oi 48.

Bugu da kari kasar ta Aljeriya ta yi suka da kakkausar murya akan ministan harkokin wajen Faransa Bruno Rotayo,tare da cewa za ta mayar masa da martanin da ya dace.

Sanarwar ma’aikatar harkokin wajen ta Aljeriya ta bayyana cewa; A matsayinta na kasa mai cikakken shugabanci, tana daukar ma’aikatan ofishin jakadanci Faransa 12 a matsayin wadanda ba a maraba da su, sannan kuma ana bukatar da su fice daga kasar a cikin sa’oi 48.”

 Aljeriya din ta dauki wannan matakin ne a matsayin mayar da martani ga kama wani jami’in diflomasiyyarta da aka yi a kasar Faransa a ranar 8 ga watan Aprilu da ake ciki.

Aljeriyan ta bayyana abinda ya faru da cewa, keta hurumin kasarta ne da kuma take dokokin aikin diflomasiyya.”

Haka nan kuma ta yi ishar da cewa, ma’aikacin diflomasiyyar da aka kama yana da kariya ta aiki wacce ta hana a yi masa abinda ya faru,amma kuma gwamnatin Faransa ta yi mu’amala a shi ta hanya mafi muni da halayya irin ta barayi.’

Alaka a tsakanin Faransa da Aljeriya tana kwan-gaba da baya, musamman a cikin watannin bayan nan. Watanni 8 da su ka gabata an sami rashin jituwa a tsakaninsu saboda korar wasu ‘yan asalin Aljeriya mazauna Faransa bisa zargin cewa sun shiga kasar ba bisa ka’ida ba. Aljeriya ta yi wa jakadanta kiranye, tare da rufe kafar diflomasiyya a tsakaninsu na tsawon watanni 8.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hajj 2025: Hukumar Alhazai Ta Shirya Taron Bita Ga Mahajjata a Jihar Kwara
  • Iran Ta Sanar Da Kasar Oman A Matsayin Wajen Tattaunawa Na Gaba Kan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Rasha Ta Sanar Da Kashe Manyan Kwamandojin Sojin Ukraine Fiye Da 60 A Birnin Sumy Na Kasar Ta Ukraine
  • Kokarin Da Iran Take A Tattaunawa Da Amurka Shi Ne Dage Mata Takunkuman Zaluncin Da Aka Dora Mata
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Zanta Da Tokwaransa Na Kasar Kuwait
  • Ministan Harkokin Noma Na Kasar Iran Ya Kama Hanya Zuwa Kasar Brazil
  •  Aljeriya Ta Kori Jami’an Diflomasiyya Faransa 12
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Allah-wadai Da Harin Jihar Filato
  • Tsangayar Ilimi Ta BUK Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa
  • Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya godewa ministan harkokin wajen kasar Omman