Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta sanar a yau Juma’a cewa, daga ranar 9 zuwa 12 ga wata, wakilin musamman na shugaba Xi Jinping, Zhang Guoqing zai tafi kasar Faransa domin halartar taron koli kan ayyukan fasahar kirkirarriyar basira ta AI, bisa gayyatar da mai karbar bakuncin taron ta yi masa.

Zhang mamba ne na ofishin siyasa na kwamitin koli na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kuma mai mukamin mataimakin firaminista a majalisar gudanarwar kasar Sin.

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lin Jian ya bayyana cewa, ta hanyar halartar taron, kasar Sin tana fatan karfafa cundayar juna da mu’amala da dukkan bangarori, da samar da daidaito kan hadin gwiwa, da kara matsa kaimi ga aiwatar da yarjejeniyar MDD kan fasahar zamani. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya ta taɓarɓare bayan mulkin IBB – Obi

Dan takarar shugaban ƙasa a Jam’iyyar Leba (LP) a zaɓen 2023, Peter Obi, ya ce Najeriya ta daɗa taɓarɓarewa fiye da lokacin da tsohon shugaban ƙasa na mulkin soja Ibrahim Badamasi Babangida ya bar mulki a shekarar 1992.

Obi ya bayyana haka ne a lokacin da yake tsokaci kan ƙaddamar da littafin tarihin Babangida da aka daɗe ana jira, mai suna ‘A Journey in Service’.

An ƙwace miliyoyin daloli, gidajen da ke da alaƙa da Emefiele ’Yan sanda sun daƙile satar mutane, sun kama wasu 3 a Borno

Aminiya ta gano cewa, ba a ba wa Obi damar shiga ba cikin zauren taron ƙaddamar da littafin ba, tare da wasu da dama da aka yi zauren taro na Congress Hall a otal din Transcorp Hotel, inda aka gudanar da taron saboda an kulle ƙofofin shiga bayan isowar Shugaba Bola Tinubu.

Obi, a saƙonsa da ya wallafa a shafin sada zumunta na X, ya bayyana cewa irin gudunmawar da IBB ke bayarwa ga tattalin arzikin Najeriya da gagarumin goyon bayansa ga harkokin kasuwanci da bunƙasar kamfanoni masu zaman kansu ba su da iyaka.

Da yake magana a kan abin da ya kira wasu muhimman abubuwa guda biyu na jawabin da IBB ya yi game da zaɓen 1993, ya ce Najeriya ba ta ci gaba ba kamar takwarorinta daga 1992 lokacin da IBB ya bar gwamnati.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya ta taɓarɓare bayan mulkin IBB – Obi
  • Jami’an Diblomasiyya Daga Kungiyar G20 Da Dama Sun Isa Afrika Ta Kudu
  • Nijar: Taron Kasa Ya Bukaci Sojoji Su Yi Mulkin Rikon Kwarya na Shekara 5
  • Wang Yi Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Uganda
  • Jakadan Sin Dake Najeriya Ya Gana Da Karamar Ministar Harkokin Wajen Kasar
  • Turkiya Ta Karbi Bakuncin Tattaunawar Sulhu Tsakanin Habasha Da Somaliya
  • Kungiyoyin Falasdinawa A Gaza Sun Bukaci Yin Taron Musamman Domin Dakile Batun Tilasa Wa Mutanen Gaza Yin Hijira
  • Shugaba Tinubu Ya Nada Sabon Shugaban Kwalejin Koyon Tukin Jiragen Sama
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa; Yahudawan Sahayoniyya Sun Kasa Murkushe Gwagwarmaya
  • Ma’aikatar sharia ta kasar Iran Ta bada sanarwan Kama Yan Kasar Burtaniya 2 Tare Da Tuhumar Leken Asiri