Kasar Iran Ta Ce; Amurka Tana Kalubalantar Cibiyoyin Kasa Da Kasa Saboda Jiji Da Kanta
Published: 8th, February 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta bayyana cewa: Amurka tana kalubalantar cibiyoyin kasashen Duniya
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya bayyana cewa: Dabi’ar Amurka ta aiwatar da dokokin cikin gida ta ketara kan iyakokinta, inda a yanzu take tunkarar cibiyoyin kasa da kasa.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya rubuta a shafin dandalin “X” dangane da sakamakon takunkumin da Amurka ta kakabawa cibiyoyin kasa da kasa misalin kotun hukunta manyan laifuka ta duniya a matsayin tarayya a tafka laifuka da gwamnatin mamayar Isra’ila, yana mai jaddada cewa: Amurka ta ketara haddinta na aiwatar da dokokin a cikin gidan kasarta, ta ketara kan iyakokinta yanzu kan cibiyoyin kasa da kasa.
Baqa’i ya kara da cewa: Kakaba takunkumi kan kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa domin gudanar da bincike kan munanan laifukan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila, wani abu ne da ba a taba ganin irinsa ba a tsawon tarihin Amurka na hada baki da wani gungun ‘yan mamaya masu nuna wariyar al’umma wadanda suke aikata muggan laifuka iri-iri ciki har da aiwatar da kisan kare dangi kan al’ummar Falastinu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Limamin Tehran: Iran Ba Ta Tsoron Tattaunawa
Wanda ya jagoranci sallar juma’a a Tehran ya bayyana cewa; Tun cin nasarar juyin musulunci, Iran ta zabi hanyar tattaunawa, saboda ta tabbatar da kyakkyawar niyyarta da kuma aiki da hankali a mu’amalrta da duniya.
Limamin na Tehran Ayatullah Saiddiki ya ce, a yayin tattaunawar da za a yi a tsakanin Iran da Amurka wacce za ta kasance ta hanyar shiga tsakani, Iran za ta ji abinda daya bangaren zai fada, sannan kuma ta bayar da jawabi, domin tabbatarwa da duniya cewa ita daula ce mai aiki da hankali, kuma ba ta tsoron tattaunawa.
Ayatullah Siddiki ya yi ishara da zancen jagoran juyin musulunci akan yadda bangaren da ake tattaunawar ba ya aiki da abubuwan da aka cimmawa da amincewa da su.
Haka nan kuma limamin na Tehran ya ambato jagoran juyin musuluncin na Iran yana bayyana yadda Amurka take kiyayya da Jamhuriyar da musulunci na Iran da addinin musulunci da kuma alkur’ani mai girma, saboda asarar manufofinta da ta yi a cikin Iran.
Ayatullah Siddiki ya kuma amabci cewa maganar da shugaban kasar Amurka yake yi na tattaunawa kai tsaye da Iran ba koma ba ne, sai yaudara da ba ta da tushe. Kuma saboda yadda Amurka ba ta aiki da duk wata yarjejeniya da aka cimmawa, don haka zama da ita gaba da gaba domin tattaunawa bai dace da mu ba.
Har ila yau, ya kuma ce, Shirin Iran na Nukiliya na zaman lafiya yana ci gaba da samun bunkasa saboda jagoranci na hikima na jagoran juyin juya halin musulunci.