Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta bayyana cewa: Amurka tana kalubalantar cibiyoyin kasashen Duniya

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya bayyana cewa: Dabi’ar Amurka ta aiwatar da dokokin cikin gida ta ketara kan iyakokinta, inda a yanzu take tunkarar cibiyoyin kasa da kasa.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya rubuta a shafin dandalin “X” dangane da sakamakon takunkumin da Amurka ta kakabawa cibiyoyin kasa da kasa misalin kotun hukunta manyan laifuka ta duniya a matsayin tarayya a tafka laifuka da gwamnatin mamayar Isra’ila, yana mai jaddada cewa: Amurka ta ketara haddinta na aiwatar da dokokin a cikin gidan kasarta, ta ketara kan iyakokinta yanzu kan cibiyoyin kasa da kasa.

Baqa’i ya kara da cewa: Kakaba takunkumi kan kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa domin gudanar da bincike kan munanan laifukan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila, wani abu ne da ba a taba ganin irinsa ba a tsawon tarihin Amurka na hada baki da wani gungun ‘yan mamaya masu nuna wariyar al’umma wadanda suke aikata muggan laifuka iri-iri ciki har da aiwatar da kisan kare dangi kan al’ummar Falastinu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran, ta yi Tir da kwamatin tsaro kan rashin tabaka komai na takawa Amurka da Isra’ila birki

Iran ta yi Allah wadai da Kwamitin Sulhun na MDD na rashin tabaka komai wajen  dakatar da ayyukan Amurka da Isra’ila wanda Iran din ta bayyana da abin kunya.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya yi tir da munanan hare-haren da jiragen yakin Amurka suka kai kan kasar Yemen da kuma yadda gwamnatin Isra’ila ke ci gaba da kai wa Falasdinawa hari a zirin Gaza, tare da yin Allah wadai da rashin daukar wami mataki daga kwamitin sulhu na fuskantar wadannan munanan ayyukan.

Esmaeil Baghaei, a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, ya bayyana matukar na dama kan yadda ake kashe fararen hula da suka hada da mata da kananan yara da ba su ji ba ba su gani ba, da kuma lalata muhimman ababen more rayuwa na kasar Yemen, sakamakon hare-haren da Amurka ke kaiwa.

Ya bayyana hare-haren da Amurka ta kai ta sama a matsayin laifukan yaki da laifukan ta’addanci, yana mai danganta hakan da “abin kunya da rashin gaskiya” na kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da sauran cibiyoyin kasa da kasa kan wannan ta’asa.

Ya ce Amurka da gwamnatin yahudawan sahyoniya sun kitsa wani shiri na hadin gwiwa na raunana al’ummar musulmi da kuma rufe duk wata muryar goyon baya ga al’ummar Falastinu da ake zalunta.

Daga karshe Baghaei ya jaddada nauyin da ya rataya a wuyan kasashen musulmi na duniya na dakatar da zaluncin da Isra’ila ke yi da kuma hare-haren da sojojin Amurka suke yi a kan Falasdinawa da sauran al’ummar musulmi, yana mai kira ga gwamnatocin musulmi da su dauki matakin da ya dace da kuma kokarin da kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC ke yi na shawo kan lamarin.

Akalla Falasdinawa 436 da suka hada da kananan yara 183 ne aka kashe tun bayan da Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza a ranar Talata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Trump Ya Bayyana Dalilin Rufe Gidan Rediyon Muryar Amurka
  • Iran da UAE sun kirayi Isra’ila da Amurka da su kawo karshen hare-harensu a Gaza da Yemen
  • Najeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Kisan Kiristoci A Kasar
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bukaci Hadin Kai Tsakanin Iraniyawa Saboda Amfanin Kasar
  • An Bukaci Shugaban Kasa Ya Sa Ido Ga Aikin Biyan Kudaden Fansho
  • Iran, ta yi Tir da kwamatin tsaro kan rashin tabaka komai na takawa Amurka da Isra’ila birki
  • Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Rahoton Amurka
  • Iran Ta Kira Jakadun Kasashen Jamus da Butaniya Zuwa Ma’aikatar Harkokin Waje Don Jan Kunnensu
  • A Jiya Laraba Ce Iran Take Bukukuwan Cika Shekaru 78 Da Kwatar Kamfanin Man Fetur Na Kasar Daga Hannun Turawan Burtaniya
  • Iran : hare-haren Isra’ila a Gaza ci gaba da kisan kare dangi ne