Rashin Aiwatar Da Sabon Tsarin Ilimi Na Kasa Na Kawo Cikas Ga Bunkasar Ilimi A Nijeriya
Published: 8th, February 2025 GMT
Su tsare tsaren anyi shirin tabbatar dukkan makarantu masu zaman kan su da na gwamnati za su fara amfani da tsarin a watan Janairu 2025.
Sai dai kuma watan Janairu ya wuce ba tare da samun wani ci gab aba dangane da lamarin. Rahoto ya nuna har yanzu da akwai sauran Rina a Kaba, domin kuwa da akwai karancin makarantu wadanda basu da irin kayan da za ayiu amfani da su wajen aiwatar da sabon tsarin,da kuma yadda za a horar da Malamai, hakan ta sa aka bar masu ruwa da tsaki cikin shakku ko sabon tsarin ilimin za afara amfani da shi.
Sabon tsarin ilimin an yi niyyar fara amfanni da shi inda za a koyar da yaddaake sabbin sana’oi na hannu 15 na karamar makarantar Firamare da sakandare inda aka yi fatan maida hankali ne kan koyawa dalibai sana’oi daban- daban, tun daga Firamare zuwa Sakandare.Sabbin sana’oin sun hada da yadda za koyi karau ta kafar sadarwa ta zaman IT, gini ta hanyar zamani ta robotics, lamarin da ya shafi aikin hotel,koyon dinki, da kuma lamarin aikin.
Duk kuwa da kwai karuwar da sabon tsarin ilimin yake tafe da ita, binciken da aka yi ta tafiye- tafiye a makarantu masu zaman kansu da kuma na gwamnati a Babban Birnin Tarayya ya nun aba da gaske ake ba lamarin fara amfani da sabon tsarin ilimi na kasa. Makarantu da dama basu shiryawa amfani da sabon tsarin ilimin ba.
Sabon tsarin ilimin an bullo da shi ne domin a samun maganin matsalolin ilim da ake fuskanta a sashen ilimi na kasar Nijeriya, abinda ya hada tsarin koyarwa na shekarun baya da suka wuce, babu abubuwan da za su taimaka wajen koyawa dalibai, da kuma yadda aka yiu wa lamarin rikon sakainar Kashi.
Hakanan ma shit sarin yayi kama da irin wanda ake yi a kasashen da suka ci gaba,inda ake koyawa ‘yan makaranta yadda za a koya masu sana’oin da za su taimaka masu matsayi na dogaro da ka,abubuwan da aka dade ana yi a kasashen duniya.Muhimman abubuwan cikin sabon tsarin ilimin inda aka kara sa wasu sabbin abubuwa a wasu darussa kamar Lissafi, kimiyya, da kuma abind a mutum zai iya koya da hannun sa, har ma da maida hankali akan fasaha a cikin azuzuwa.
Gwamnati ta yi alkawarin za ta bada duk taimakon da ya kamata domin a tabbatar da cewa an samu fara aiki da sabon tsarin ilimi, sai dai kuma su alkawuran sun ba haka aka yi tsammanin lamarinzi kasance ba, kowa lamarin ya ba shi mamaki.
Irin wannan abin ya sa mutane da damar ansu ya baci kuma abin ya basu kunya daga cikin wadanda suke da ruwa da tsaki,wadanda suke ganin koma baya irin hakan, yana kara taazzara lamarin ne na matsalolin ilimi ne da ‘yan Nijeriya suka dade da fuskanta.
কীওয়ার্ড: da sabon tsarin ilimi sabon tsarin ilimin
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa ta ƙaddamar da shirin noman rani na Lallashi
A kokarin Gwamnatin Jihar Jigawa na karfafa ayyukan noman rani tare da samar da wadataccen abinci da inganta rayuwa, ta kaddamar da shirin noman rani na Lallashi da ake amfani da rijiyoyin burtsatse a Karamar Hukumar Maigatari ta jihar.
Rahoton na nuna cewa, an yi aikin ne domin canza salon noman rani da sauran ayyukan noma a yankunan da galibi hamada ce.
A cewar rahoton, wannan shiri ana yin amfani da makamashin hasken rana da kuma amfani da na’urori masu rahusa tare da dabarun noman rani don samar da harkokin noman rani mai inganci cikin sauki.
Dakatar da Gwamnan Ribas zubar da ƙimar Nijeriya ne a idon duniya — Jonathan An ayyana zaman makoki na kwana uku bayan kashe mutum 44 a NijarDa yake jawabi a lokacin kaddamar da aikin, Gwamna Umar Namadi ya bayyana muhimmancin aikin, inda ya bayyana hakan a matsayin wata hanya ta jaddada kudirin gwamnatinsa na ganin an samar da abinci mai yalwa da samar da hanyoyin rayuwa mai dorewa da rage radadin talauci a tsakanin al’umma.
Ya kuma bayyana cewa, babban abin da gwamnatinsa ta sanya a gaba shi ne na cimma manufofin kudirorinta 12 wajen amfani da hanyoyin noma na zamani a Jihar Jigawa, musamman ta hanyar gudanar da ayyukan noma a duk shekara.
Ya kara da cewa, gwamnatinsa na daukar matakai daban-daban don gyara da fadada wuraren noman rani a fadin jihar da suka hada da samar da madatsun ruwa da rijiyoyin burtsatse na yau da kullum.
Sai dai an bayyana cewa shirin noman na Lallashi da rijiyar burtdatse ya kunshi gonaki hekta 10 kuma yana samun tallafin manyan rijiyoyin burtsatse irin na masana’antu guda hudu, kuma ya zuwa yanzu, manoma sama da 80 ne ke cin gajiyar shirin kai-tsaye, wanda ake sa ran zai bunkasa noman sosai da kuma yaukaka tattalin arziki.
Da yake jawabi a madadin manoman yankin, malam Aliyu Musa ya bayyana cewa, abin da gwamnati ke yi wa al’ummomin da ke kewayen wurin noman rijiyoyin burtsatse tamkar jari ta bayar na rayuwa da ba za a iya tantance adadinsa ba.
A cewarsa, jama’a za su ci gaba da addu’o’in samun nasarar shirin tare da fadada shirin domin kara fadada shi a yankunan jihar gaba daya.
“Da farko mutanen wannan yanki suna yin noman rani ne da zarar lokacin damina ya kare, amma labarin ya canza a yanzu, wanda ke nufin ba za a bar kauye zuwa birni ba don ci-rani.
“Nan ba da dadewa ba birni zai zo gare mu, yayin da muka fara nazarin wannan dama mai albarka ta tashi a matsayin al’ummomin da ke da wuraren noman rani,” inji shi.