Kasashe 79 Sun Yi Watsi Da Matakin Trump Na Kakabawa Kotun ICC Takunkumi
Published: 8th, February 2025 GMT
Kasashe 79 na duniya sun yi watsi da matakin da shugaban kasar Amurka Donald Trump ya dauka na kakabawa kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC takunkumi, suna masu cewa matakin na raunana tsarin dokokin kasa da kasa.
Wadannan kasashen da suka hada da Canada, Jamus, Faransa, Afirka ta Kudu da kuma Mexico, a wata sanarwar hadin gwiwa na cewa irin wadannan matakan na kara barazanar rashin hukunta masu manyan laifuka.
Har ila yau a cikin sanarwar, kasashen 79 sun jaddada cewa takunkumin da Amurka ta kakabawa kotun ta ICC na iya yin illa ga sirrin bayanan da suka shafi wadanda abin ya shafa, da shaidu da kuma jami’an shari’a, wadanda ‘yan asalin wadannan kasashe ne.
Sanarwar ta zo ne sa’o’i bayan da Trump ya sanya hannu kan wani umarni na zartarwa na sanya takunkumi na kudi da hana biza ga ma’aikatan ICC da iyalansu.
A sanarwar hadin gwiwa da kasashen sun nuna yin nadamar duk wani yunkuri na kawo cikas ga ‘yancin cin gashin kan kotun.
Shugaban Amurka Donald Trump a ranar Alhamis ya ba da izinin kakaba takunkumin tattalin arziki da tafiye-tafiye kan mutanen da ke aiki kan binciken kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa da ya shafi ‘yan kasar Amurka ko kawayenta irinsu Isra’ila.
Matakin dai ya zo daidai da ziyarar da firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu wanda kotun ICC ke nema ruwa a jallo dangane kan aikata laifukan yaki a zirin Gaza, ke ziyara a Amurka, saidai kotun ta yi ICC, ta ce wannan matakin ba zai katse mata hamzari ba wajen gudanar da aikinta.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
Haka zalika, Kangye ya kuma tabbatar wa da al’umma cewa; jami’an tsaro na ci gaba da mayar da hankali wajen cafke fitaccen shugaban ‘yan ta’addan nan, Bello Turji.
Sannan, ya yi watsi da ikrarin da sojoji suka yi na cewa; sun dakile hare-haren makiyaya da ‘yan ta’adda da kuma barayin shanu da sauran makamantansu.
Da yake yin jawabi game da kyautata wa sojojin da suka jikkata, Kangye ya musanta zargin yin watsi da sojojin da suka samu raunuka.
Ya ce, “To, a iya sanina dangane da abin da hukumar sojoji ke yi, sojojinmu na samun isasshiyar kulawa, kuma kai dan jarida ne, da ka lura da lokacin hutun Sallah, za ka ga yadda babban hafsan soji da hafsan hafsoshin sojin sama da wasu manyan hafsoshi daga hedikwatar hukumar suka ziyarci sojojin, domin taya su murnar Sallah.
“Sannan kuma, zan iya fada muku cewa; hedikwatar rundunar sojojin Nijeriya, na kula da marasa lafiya da wadanda suka samu raunuka da wasu da ke bukatar a fitar da su zuwa kasashen waje, ana fitar da su, domin nema musu lafiya; wasu sun tafi Masar, wasu Turkiyya, wasu kuma Kasar Indiya. Kamar yadda muke magana yanzu, wasu har yanzu suna can suna samun kulawar likitoci a can.”
Ya kuma bayyana cewa, a ‘yan watannin da suka gabata, an raba wa sojojin da suka samu jikkata a fagen-daga gidaje.
Kangye ya kuma yi nuni da cewa, an raba wa sojojin da suka jikkatan gidajen kyauta ne, domin kuwa wasu daga cikinsu; ba za su iya dawowa fagen aiki ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp