HausaTv:
2025-04-14@20:40:09 GMT

Trump Ya Bada Umurnin Rage Tallafin Da Amurka Ke Ba Afrika Ta Kudu

Published: 8th, February 2025 GMT

Shugaban Amurka Donald Trump ya rattaba hannu a kan dokar da za ta rage tallafin da Amurka ke baiwa Afirka ta Kudu, wanda ake ganin bai rasa nasaba da karar Isra’ila da Afrika ta Kudu ta shigar kan kisan gilla a Zirin Gaza da kuma kwace filaye

A ranar Juma’a ne fadar White House ta Amurka ta tabbatar da cewa Trump ya rattaba hannu kan wani kudiri na yanke tallafin kudi ga Afirka ta Kudu, saboda rashin amincewarsa da manufofinta na filaye, har ma da batun shigar da kara kan kisan gillar da ta yi a kotun kasa da kasa (ICJ) kan Isra’ila.

Gwamnatin Trump ta ba da misali da shari’ar da Afrika ta kudu ta jagoranta kan Isra’ila a kotun ICJ a watan Disamba na 2023, kan Washington da kawayenta.

Fadar White House ta kuma ce gwamnatin Trump za ta tsara wani shiri na sake tsugunar da manoman farar fata na Afirka ta Kudu da iyalansu. –

Trump dai bai bayar da wata shaida kan zargin da ya yi wa gwamnatin Afirka ta Kudu ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jiragen Saman Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Luguden Wuta Kan Asibitin Baptist Da Ke Gaza

Jiragen saman yakin mamayar Isra’ila sun kai farmaki kan asibitin Baptist da ke birnin Gaza, lamarin da ya janyo dakatar da aiki a cikinsa

Wakilin gidan talabijin na Al-Alam Mohammed Al-Balbisi ya ruwaito cewa: Jiragen saman yakin sojojin mamayar Isra’ila sun yi ruwan bama-bamai a wasu gine-gine na asibitin Baptist, da suka hada da ginin sashin kula da marasa lafiya cikin gaggawa da kuma motocin daukar marasa lafiya da wasu sassa da tantuna da ke ba da hidima ga wadanda suka jikkata.

Ya yi nuni da cewa da sanyin Safiya yau Lahadi, sojojin mamayar Isra’ila sun harba makamai masu linzami da dama kan wadannan gine-gine lamarin da ya tilastawa marasa lafiya da likitoci ficewa daga asibitin tare da fakewa a nesa da asibitin, inda hare-haren suka rusa gine-ginen asibitin.

Wakilin ya kara da cewa: Wannan shi ne karo na biyu da ake kai wa asibitin Arab Baptist hari, domin an kai harin bama-bamai a farkon fara kai hari kan Gaza, wanda ya yi sanadin mummunan kisan kiyashi da ya ci rayukan daruruwan mutane.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Guguwar Kudin Fito Na Gwamnatin Trump: Dabara Ko Hauka?
  • Hamas ta ce a shirye take ta sako dukkan fursunonin Isra’ila da suka rage, domin musanya fursunoni”
  • Gwamna Namadi Ya Bada Ai hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.
  • Jiragen Saman Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Luguden Wuta Kan Asibitin Baptist Da Ke Gaza
  • Zulum Ya Gana Da Yaron Da Aka Ci Zarafi, Ya Ba Shi Gida, Tallafin Karatu
  • HKI Ta Jefa Boma-Bomai A Kan Asbiti Tilo Da Ya Rage Yake Aiki A Arewacin Gaza
  • Sama da mutane 1,560 ne sukayi shahada tun bayan da Isra’ila ta koma kai farmaki Gaza
  • Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Amurka da Iran
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • Iyaye Mata Sun Bukaci A Rika Samar Da Kayayyakin Bada Tazarar Haihuwa Akan Lokaci