Za’ayi Musayar Fursunoni Ta Biyar Tsakanin Isra’ila Da Hamas
Published: 8th, February 2025 GMT
Isra’ila za ta saki fursunonin Falasdinawa 183 yau Asabar, a madadin wasu mutanenta uku daga cikin wadanda kungiyar Hamas ke garkuwa da su a Gaza a wani bangare na aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza da suka cimma.
Kamar dai a makon da ya gabata, za a yi musaya ta biyar a wurare biyu a zirin Gaza a jere inji rahotanni.
A maimakon haka, Isra’ila za ta saki fursunonin Falasdinawa 183, ciki har da 18 da aka yanke wa hukuncin daurin rai da rai, ciki har da wasu fitattun mutane irin su Iyad Abu Shidam, wanda Isra’ila ta yankewa hukuncin daurin rai da rai a Beersheva a shekara ta 2004.
Bayanai sun ce kimanin 111 daga cikin wadannan fursunonin ‘yan Gaza ne da ake tsare da su tun ranar 7 ga watan Oktoba.
Wannan dai shi ne karo na biyar da ake gudanar da musayar irin wannan tun bayan da yarjejeniyar tsagaita bude wuta a zirin Gaza ta fara aiki a ranar 19 ga watan Janairu, bayan shafe watanni goma sha biyar ana yakin na Gaza.
Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu zai sa ido kan musayar tun daga Amurka, inda ya fara wata ziyara a ranar Litinin, kamar yadda ofishinsa ya bayyana.
Tun bayan fara tsagaita wutar, an sako wadanda ake garkuwa dasu 18 da da fursunonin falasdinawa 582.
Kashi na farko na yarjejeniyar, wanda zai dauki tsawon makonni shida, ya tanadi mikawa Isra’ila jimillar mutane 33 da aka yi garkuwa da su, ciki har da akalla takwas da suka mutu, a madadin Falasdinawa 1,900.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Da Prabowo Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Sin Da Indonesiya
A yau Lahadi ne shugaban kasar Sin Xi Jinping da shugaban kasar Indonesia, Prabowo Subianto suka yi musayar taya juna murnar cika shekaru 75 da kulla huldar diplomasiyya tsakanin kasashen biyu. Inda shugaba Xi ya ce, yana dora matukar muhimmanci kan raya dangantakar dake tsakanin Sin da Indonesia, kuma a shirye yake ya yi amfani da bikin cika shekaru 75 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu, a matsayin wata dama ta yin aiki tare da shugaba Prabowo, wajen kara zurfafa hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare, da karfafa hadin gwiwa a batutuwan da suka shafi bangarori daban daban bisa manyan tsare-tsare, da ci gaba da inganta al’ummar Sin da Indonesiya mai kyakkyawar makomar bai daya daga dukkan fannoni, kuma bisa yanayin sabon zamani, da kafa misali na hadin kai da amincewa da juna tsakanin manyan kasashe masu tasowa, da zama abin koyi na ci gaban hadin gwiwar bai daya ga kasashe masu tasowa, ta yadda za su ba da gudummawa tare wajen ci gaban dan Adam.
A nasa bangaren, Prabowo ya bayyana fatan bangarorin biyu za su ci gaba da zurfafa hadin gwiwa tare da tabbatar da zumunci a tsakanin al’ummomin kasashen biyu, ta yadda za su ba da gudummawa mai kyau ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp