Aminiya:
2025-04-14@17:18:49 GMT

An dakatar da dagaci kan zargin saran maraya da adda

Published: 8th, February 2025 GMT

An dakatar da Dagacin Karagawal da ke Jihar Gombe, Usman A. Bello, daga kujerarsa, har sai an kammala bincike kan zargin da ake masa na saran wani maraya da adda har sau bakwai.

A baya Aminiya ta ruwaito yadda jikin marayan, mai suna Adamu Muhammad mai shekara 15 ya fara ɗoyi saboda rashin samun kulawa bayan asibiti sun ƙi karbarsa saboda rashin kuɗi, sakamakon raunukan da yake zargin dagacin ya yi masa.

A yayin hirar da Aminiya ta yi da shi a lokacin, Dagacin ya musanta sarar yaron, inda ya bayyana cewa ya yi ƙoƙarin kare kansa ne bayan varayi ɗauke da makami sun shiga gidansa.

Lamarin da ya faru a farkon watan Disamba na shekarar 2024, wanda ya haifar da ce-cekuce a yankin.

‘A sansanin gudun hijira na yi sakandare har na zama likita’ Jirgin Amurka ɗauke da mutum 10 ya ɓace

Shugaban Ƙaramar Hukumar Gombe, Barista Sani A. A. Haruna, ya bayyana cewa an dakatar da basaraken ne domin tabbatar da adalci da kuma kare martabar duk wanda lamarin ya shafa.

Ya ce, “Mun ɗauki xawainiyar jinyar yaron, inda muka kashe sama da Naira dubu ɗari biyar. Wannan nauyi ne na gwamnati, ba iyayensa ba, domin ba shi ya ji wa kansa ciwo ba.”

Barista Haruna ya ce an dakatar da Dagacin ne bayan ƙorafin da aka samu cewa ya ɗauki matakin da ya saba wa doka, “ko da yaron ya aikata wani laifi, ba ya halatta a xauki doka a hannu. A maimakon haka, doka ta tanadi cewa a kai shi gidan horon yara. Amma abin da ya fi muhimmanci a yanzu shi ne tabbatar da cewa yaron ya samu sauqi kafin a ci gaba da bincike.”

Dagacin Karagawal, Usman A. Bello, ya kare kansa da cewar wasu matasa ne suka shiga gidansa da makamai cikin dare da nufin sata, wanda hakan ya sa shi ɗaukar matakin kare kansa.

Ya ce, “Na samu nasarar qwace adda daga ɗaya daga cikinsu, sannan na yi amfani da ita don kare kaina.’

A daya bangaren, saurayin aka yi wa raunin, Adamu Muhammad, ya musanta daukar makami ko aikata sata. Ya ce, “Na shiga gidan ne ba tare da izini ba, amma Dagacin ne ya zo da adda ya sassara ni har na ji ciwo a wurare daban-daban.”

Idan ba a manta ba, a baya yaron ya shaida wa wakilin Aminiya cewa ya je neman mafaka a gidan dagacin ne saboda tsoron matakin da mahaifiyarsa za ta xauka a kansa bayan ya yi faɗa da wata budurwa a makwabtansu, har ta kai ƙararsa wurin ’yan banga, suka nemi ya biya yarinyar kuɗi, kuma ba shi da su.

Shugaban ƙaramar hukumar ya ce za a gudanar da cikakken bincike ba tare da nuna son kai ba. Ya ce, “Ba za mu yanke hukunci yanzu ba, har sai mun saurari bayanin yaron da zarar ya samu lafiya.

“Idan aka yanke hukunci yanzu kuma daga baya wani abu ya taso, misali rashin lafiyarsa ko wani akasin haka, to shari’ar za ta canza gaba ɗaya.”

Ya kara da cewa matakin dakatar da Dagacin ya ba da damar gudanar da bincike cikin gaskiya da adalci. “Idan bincike ya tabbatar da cewa Dagacin ne ya yi wa yaron rashin adalci, to za a xauki matakin da ya dace. Idan kuma aka gano cewa yaron ne da laifi, za a yi hakan cikin tsari.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Karagwal

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu ta tsare ’yan TikTok 2 a Kano

Wata Kotun Majistire mai lamba 7 a Kano, ta bayar da umarnin tsare wasu ’yan TikTok biyu kan zargin wallafa wasu bidiyon batsa a shafukansu na dandalin sada zumunta.

Hukumar Tace Fina-Finai ta Kano ce ta gurfanar da ababen zargin biyu — Isa Kabir Brigade da Fatima Adam Kurna — kan wallafa bidiyon da suka saɓa wa tarbiyya da addini.

An rantsar da shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Katsina ’Yar shekara 66 ta haifi ɗanta na 10 da kanta

Sai dai bayan lauyan da ke ɓangaren masu shigar da ƙara, Garzali Maigari Bichi ya karanta musu ƙunshin tuhume-tuhumen, sun musanta wasu daga ciki.

Dangane da hakan ne Alƙalin Kotun, Halima Wali ta bayar da umarnin tsare ababen zargin tare da ɗage zaman kotun zuwa ranar 24 ga watan Afrilu.

Ana iya tuna cewa dai Hukumar Tace Fina-Finai ta Kano ta ɗaura ɗamarar tsaftace dandalan sada zumunta ta hanyar kame da ladabtar da masu wallafe-wallafen duk wani abu da ya ci karo da tarbiyya da addini.

Ko a bayan nan sai da hukumar ta gurfanar da wasu mutum biyu — waɗanda aka yankewa hukuncin ɗauri na shekara guda ko zaɓin biyan tara ta Naira dubu 100 — kan wallafa bidiyon batsa a shafukansu na TikTok.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu ta tsare ’yan TikTok 2 a Kano
  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa
  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin Ɓarayin Wayar Wutar Lantarki Ne A Yobe
  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Dakatar Da Matakin Kare-Karen Harajin Fito Kan Hajojin Da Ake Shigarwa Kasar
  • Iran Zata Yaye Labulen Ire-Iren Makamanta Na Musamman Da Ta Mallaka Domin Kare Kai
  • Zulum Ya Gana Da Yaron Da Aka Ci Zarafi, Ya Ba Shi Gida, Tallafin Karatu
  • Mahaifi ya yi wa ’yarsa ciki a Bauchi
  • Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi
  • Sin: Idan Har Amurka Na Son Tattaunawa, Ya Zama Wajibi Ta Dakatar Da Aiwatar Da Matakan Gangaci
  • An kashe mutum kan zargin satar kare a Bauchi