An dakatar da dagaci kan zargin saran maraya da adda
Published: 8th, February 2025 GMT
An dakatar da Dagacin Karagawal da ke Jihar Gombe, Usman A. Bello, daga kujerarsa, har sai an kammala bincike kan zargin da ake masa na saran wani maraya da adda har sau bakwai.
A baya Aminiya ta ruwaito yadda jikin marayan, mai suna Adamu Muhammad mai shekara 15 ya fara ɗoyi saboda rashin samun kulawa bayan asibiti sun ƙi karbarsa saboda rashin kuɗi, sakamakon raunukan da yake zargin dagacin ya yi masa.
A yayin hirar da Aminiya ta yi da shi a lokacin, Dagacin ya musanta sarar yaron, inda ya bayyana cewa ya yi ƙoƙarin kare kansa ne bayan varayi ɗauke da makami sun shiga gidansa.
Lamarin da ya faru a farkon watan Disamba na shekarar 2024, wanda ya haifar da ce-cekuce a yankin.
‘A sansanin gudun hijira na yi sakandare har na zama likita’ Jirgin Amurka ɗauke da mutum 10 ya ɓaceShugaban Ƙaramar Hukumar Gombe, Barista Sani A. A. Haruna, ya bayyana cewa an dakatar da basaraken ne domin tabbatar da adalci da kuma kare martabar duk wanda lamarin ya shafa.
Ya ce, “Mun ɗauki xawainiyar jinyar yaron, inda muka kashe sama da Naira dubu ɗari biyar. Wannan nauyi ne na gwamnati, ba iyayensa ba, domin ba shi ya ji wa kansa ciwo ba.”
Barista Haruna ya ce an dakatar da Dagacin ne bayan ƙorafin da aka samu cewa ya ɗauki matakin da ya saba wa doka, “ko da yaron ya aikata wani laifi, ba ya halatta a xauki doka a hannu. A maimakon haka, doka ta tanadi cewa a kai shi gidan horon yara. Amma abin da ya fi muhimmanci a yanzu shi ne tabbatar da cewa yaron ya samu sauqi kafin a ci gaba da bincike.”
Dagacin Karagawal, Usman A. Bello, ya kare kansa da cewar wasu matasa ne suka shiga gidansa da makamai cikin dare da nufin sata, wanda hakan ya sa shi ɗaukar matakin kare kansa.
Ya ce, “Na samu nasarar qwace adda daga ɗaya daga cikinsu, sannan na yi amfani da ita don kare kaina.’
A daya bangaren, saurayin aka yi wa raunin, Adamu Muhammad, ya musanta daukar makami ko aikata sata. Ya ce, “Na shiga gidan ne ba tare da izini ba, amma Dagacin ne ya zo da adda ya sassara ni har na ji ciwo a wurare daban-daban.”
Idan ba a manta ba, a baya yaron ya shaida wa wakilin Aminiya cewa ya je neman mafaka a gidan dagacin ne saboda tsoron matakin da mahaifiyarsa za ta xauka a kansa bayan ya yi faɗa da wata budurwa a makwabtansu, har ta kai ƙararsa wurin ’yan banga, suka nemi ya biya yarinyar kuɗi, kuma ba shi da su.
Shugaban ƙaramar hukumar ya ce za a gudanar da cikakken bincike ba tare da nuna son kai ba. Ya ce, “Ba za mu yanke hukunci yanzu ba, har sai mun saurari bayanin yaron da zarar ya samu lafiya.
“Idan aka yanke hukunci yanzu kuma daga baya wani abu ya taso, misali rashin lafiyarsa ko wani akasin haka, to shari’ar za ta canza gaba ɗaya.”
Ya kara da cewa matakin dakatar da Dagacin ya ba da damar gudanar da bincike cikin gaskiya da adalci. “Idan bincike ya tabbatar da cewa Dagacin ne ya yi wa yaron rashin adalci, to za a xauki matakin da ya dace. Idan kuma aka gano cewa yaron ne da laifi, za a yi hakan cikin tsari.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Karagwal
এছাড়াও পড়ুন:
Wakilin Sin Ya Yi Bayani Game Da Tunanin Sin Kan Kare Hakkin Dan Adam Da Kin Amincewa Da Siyasantar Da Hakkin Dan Adam
Zaunannen wakilin Sin dake ofishin MDD a Geneva da sauran kungiyoyin kasa da kasa a kasa Switzerland Chen Xu ya yi jawabi a gun taron hukumar kare hakkin dan Adam ta MDD karo na 58 kan batun kare hakkin dan Adam na kasa da kasa, inda ya yi bayani game da tunanin Sin kan kare hakkin dan Adam da kin amincewa da siyasantar da batutuwan da suka shafi hakkin dan Adam.
Chen Xu ya yi nuni da cewa, ana bukatar bin ra’ayin bangarori daban daban da tunanin kare hakkin dan Adam da yin hadin gwiwa mai amfani don sa kaimi ga raya sha’anin kare hakkin dan Adam. Wasu kasashe sun yi amfani da dalilin kare hakkin dan Adam wajen tsoma baki cikin harkokin cikin gida na wasu kasashe, da yin amfani da ma’auni biyu, da tada rikice-rikice, da kuma kakabawa wasu takunkumi daga bangare daya. Wadannan kasashe sun kau da kai daga yanayinsu na keta hakkin dan Adam, da maida kansu a matsayin alkalan kare hakkin dan Adam, da zargin wasu kasashe kan yanayin kare hakkin dan Adam, sun kawo illa ga tsarin kare hakkin dan Adam na MDD.
Chen Xu ya kara da cewa, kasar Sin ta tsaya tsayin daka kan tunanin kare hakkin dan Adam bisa tushen kyautatawa jama’a, da kiyaye tabbatar da moriyar jama’a. Kasar Sin tana girmama jama’ar sauran kasashe wajen zabar hanyar raya hakkin dan Adam da kansu, da kuma samar da gudummawa wajen raya tsarin siyasa na duk dan Adam baki daya. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp