Yadda Za Ku Magance Kaikayin Gaba
Published: 8th, February 2025 GMT
Yadda ake amfani da shi:
Za ku dinga shafa zumar a gabanku, ku barta na tsawon mintuna 30, sai ku wanke da ruwan dumi, sannan ku shafa Man Zaitun. Za ku dinga yin haka safe da yamma kafin kwanciya.
Sannan ku dinga dafa ‘ya’yan hulba na tsawon mintuna 10 da ruwan da bai wuce kofi daya ba, sai ku dora shi a wuta ya dan tafasa bayan kun sauke shi sai ku tsiyaye shi sai ku sa masa zuma cokali uku, za ki yi wannan hadin shima safe da yamma.
Sai kuma maganin kurajen da kaikayin gaba:
Kai tsaye ana cewa sanyin mara shi ne yake jawo wannan matsala, amma abin da ya kamata mu sani shi ne ba iya shi kadai yake jawowa ba akwai abubuwa da dama.
Akwai abubuwa da yawa da ke haifar da wannan matsala, bayan kamuwa da cuta da akan ce yana haifar da wannan matsalar, akwai wasu abubuwa a bayansa.
Wani lokacin sanya kaya ko ‘Underwear’ wanda ya matse ka yana jawo kaikai wani kuma motsa jiki ko tafiya mai nisa a kafa ko gudu suna jawo masa wannan.
Akwai karancin tsafta, mutum ya rika sanya ‘Underwear’ kusan mako guda ba tare da an canza shi ba, wasu kuma ba sa barinsu su bushe bayan sun yi wanka sannan su sanya tufafi, duk suna haifar da wannan matsala.
Koda gaban dadewa yake yana saba yana wari in sha Allah idan akai wannan za’a samu waraka
Abubuwan da ake bukata:
Man Darbejiya, Man tafarnuwa, Man zogale, Man kwakwa:
Yadda ake hadawa:
Da farko za ku samu kowanne daga cikinsu, amma ku tabbata kun samu na asali masu kyau saboda biyan bukata, kuma kowanne yana samuwa a Islamic chemist.
Idan kuka saya kowanne, ku auna shi da murfin kwalbar.
Sai a hada su waje daya a shafa a wurin da kurajen ya bayyana ga namiji, idan ya takura sai a bar shi, sai a yi wanka a bar shi ya bushe, sai a shafa wannan maganin a wurin sannan a sa tufafi, sai a yi kokarin canza rigar a kowane kwana 2.
Idan mace tana da kuraje ko kamuwa da cuta na dogon lokaci ko kamuwa da cuta, sai ta samu auduga ta shafa mai a jikinta idan ta kwanta ta danna gabanta kuma a sha ruwan dumi, a guji shan ruwan sanyi. Allah ya sa mu dace.
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano Za Ta Sake Buɗe Makarantun Kwana 10 Don Inganta Ilimin Yara Mata
Ta bayyana cewa gwamnatin jihar ta bayyana ayyana dokar ta-ɓaci a harkar ilimi, kuma ta kashe biliyoyin Naira wajen gyara da sabunta makarantun kwana, inda ta ce “nan ba da jimawa ba za a sake buɗe su don yara mata su ci gaba da samun ilimi.”
Ta kuma ƙara da cewa wasu daga cikin makarantun da ke aiki kamar WTC Kano da GGS Dala na karɓar yara daga yankunan da ke kewaye da su, kuma za a yi amfani da irin wannan tsari a sauran makarantun da za a sake buɗewa.
Hajiya Amina ta ƙara da cewa ofishinta ya samu amincewa daga ma’aikatar don gudanar da bincike a wasu yankuna da ke fama da yawan yara mata da ba sa zuwa makaranta ko kuma waɗanda suka daina karatu, don gano matsalolinsu da kawo mafita.
A nasa ɓangaren, Abdulaziz Musa, wanda shi ne mai kula da shirin “Bridging Access to Girls Education” na BCAI, ya bayyana cewa manufar taron ita ce tattauna ci gaba da ƙalubale da kuma amfani da kuɗaɗen da aka ware don ilimin ’yan mata tare da wakilan gwamnati, ƙungiyoyin fararen hula, da kuma ’yan jarida.
Ya ce duk da ci gaban da aka samu, har yanzu akwai ƙalubale mai yawa, don haka akwai buƙatar haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da ƙungiyoyi masu zaman kansu domin ciyar da harkar gaba.
Ya ƙara da cewa sun samar da wani tsarin kasafin kuɗi da ya dace da buƙatun mata wanda gwamnati za ta iya amfani da shi wajen tsara yadda za a kashe kuɗin da aka ware don inganta ilimin yara mata a Jihar Kano.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp