Aminiya:
2025-04-15@15:47:14 GMT

Yadda rikicin shugabanci ya janyo rufe babban masallacin gari

Published: 8th, February 2025 GMT

A bayan nan ne mahukunta a Ƙaramar Hukumar Agege, a ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙaramar Hukumar Agege, Alhaji Ganiyu Kola Egunjobi suka kulle babban masallacin Hausawa na garin, biyo bayan wani rikici da ke da alaƙa da na limanci ya ɓarke a masallacin a ranar Juma’a makon jiya.

Rikicin na zuwa ne bayan rasuwar babban limamin garin Agege, Shaikh Sharif Habib Abdul-Majid, wanda ya rasu kwanaki biyu gabanin aukuwar lamarin.

Yadda Kano ke samar da madarar Naira biliyan 2.2 An dakatar da dagaci kan zargin saran maraya da adda

A wani bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta na zamani, an ga masallata a cikin masallacin suna kai wa junansu duka, wadanda suka haɗar da ɓangarori uku.

Waɗanda suka bai wa hammatar iska sun haɗa da ɓangaren gidan limamin da ya rasu da magoya bayansu da kuma ɓangaren gidan Na’ibinsa tare da magoya bayansu, waɗanda ke fatan Na’ibin ya zama limamin gari sai kuma ɓangaren Masarautar Agege da magoya bayan masarautar.

Shaikh Mahmud Shafi’i, Baba Addini na ‘yan Arewa mazauna Legas wanda yake ɓangaren da ke fafutukar ganin Shaikh Mustapha Imam Mukhtar ya zama limamin garin Agege, domin a cewarsa shi ne Na’ibi ya shaida wa Aminiya cewa, a kan idonsa rikicin masallacin ya ɓarke a ranar Juma’a.

Ya ce bayan da Na’ibin masallacin ya shigo zai hau mumbari ne sai magoya bayan ɗan limamin masallacin da aka tanadar tare da wasu ‘yan agaji da suka hana shi hawa mumbari nan da nan kuma aka shigo da ɗan limamin da ya rasu shaikh Sharif Isma’il Habib, wanda ya ba da sallah a lokacin da ake tsaka da hayaniya.

Mustapha Imam Mukhtar ya ƙara da cewa, “an taɓa kulle masallacin ne tun a lokacin anobbar Korona, bayan barkewar wani rikici.

“Amma a wancan lokacin an cim ma yarjejeniya bayan wani zaman sulhu da sasanci da majalisar jihar ta yi da ɓangarorin da al’amarin ya shafa, inda aka cim ma daidaiton cewa, Marigayi Shaikh Sharif Habib shi ne limamin masallacin.

“Sai kuma Shaikh Mustapha Imam Mukhtar da aka tabbatar Na’ibi, kuma aka ce ba zai yiwu ɗansa ya zama Na’ibi ba, domin ba zai yiwu ba yana limanci ɗansa kuma Na’ibi ba, wanda a kan wannan yarjejeniya ake, don haka tunda liman ya rasu a ka’ida Na’ibinsa ne zai zama limamin gari, ya ci gaba da bada salla, sai dai abun takaici ne abun da ke faruwa a yanzu,” in ji shi.

Aminiya ta tuntuɓi magatakardar Masarautar Agege, Alhaji Abubakar Ali Na’ibi, wanda ya ce duk garin da ke samun ci gaba da bunƙasa ba a raba shi da irin wannan rigingimu.

Ya ce, Masarautar Agege ita ke da alhakin gudanar da al’amuran babban masallacin garin.

“Wannan al’ada haka take a ko’ina a kasar Hausa, babban masallacin gari yana ƙarƙashin kulawar masarauta ce, kuma haka abun yake a garin Agege tun fil azal, kuma Masarautar Agege ɗan marigayi limamin gari, Shaikh Sharif Isma’il Habib ta sani a matsayin Na’ibi, shi ne wanda ta naɗa Na’ibi tun da daɗewa, kuma shi ne ta sani ni a matsayin limamin gari,” in ji shi.

A wata sanarwa da Shugaban Karamar Hukumar Agege ya fitar a shafinsa na kafafen sada zumunta na zamani ya ce, matakin rufe masallacin ya zama tilas domin kare afkuwar rikici, inda ya shaida cewa, zai gayyato dukkanin ɓangarorin da ke rikici domin a zauna a teburin sulhu.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hausawa Jihar Legas Masarautar Agege Masarautar Agege Shaikh Sharif limamin gari magoya bayan

এছাড়াও পড়ুন:

’Yar shekara 66 ta haifi ɗanta na 10 da kanta

Wata ’yar kasar Jamus mai suna Alexandra Hildebrandt mai shekara 66 ta ja hankalin jama’a bayan ta haifi ɗanta na 10 ba tare da maganin haihuwa ba.

Haihuwar ta faru ne a ranar 19 ga Maris a Asibitin Charité da ke Berlin da taimakon likita.

Bello Turji ya kashe manoma 11 a Sakkwato ’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato

Ta bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da ta yi da Jaridar TODAY.com a ranar Laraba, 26 ga watan Maris.

A cewar Hildebrandt, ta rawa wa jaririn suna Philipp, wanda ya zo da nauyin kilo 7, kuma yana cikin koshin lafiya.

Ta bayyana shi a matsayin wanda ya dace da ’ya’yanta da ke da yawa, wanda ya haɗa da yara masu shekaru tsakanin 2 zuwa 46.

“Babban iyali ba kawai wani abu ne mai ban mamaki ba, amma duk da haka, yana da mahimmanci don renon yara yadda ya kamata,” in ji ta a cikin imel.

Hildebrandt, wanda ke kula da gidan tarihi na Wall Museum a Checkpoint Charlie a Berlin, ba bakon abu ba ne wajen jan hankalin jama’a.

Rayuwarta cike take da tarihi, domin zama uwa a wurinta abin mamaki ne.

Duk da shekarunta, ta nace cewa ciki ba a tsara shi ta hanyar kimiyya, amma ya faru ne ta dabi’a.

Mahaifiyar ta bayyana cewa, tana rayuwa cikin matukar aiki.

Kafin haihuwar Philipp, ta bayyana wa Jaridar Jamus ta Bild cewa, “Ina cin abinci cikin koshin lafiya, ina iya yin ninkaya tsawon awa guda a matsayin motsa jiki kuma ina tafiyar tsawon awa biyu.”

Likitanta, Dokta Wolfgang Henrich ya tabbatar da cewa, cikin nata ya daidaita, yana mai bayyana shi a matsayin cikin da ba shi da matsala sosai,” kodayake Hildebrandt ta yi haihuwa takwas a baya duk ta hanyar tiyata.

‘Ya’ayanta 10 sun hada da tagwaye, Elisabeth da Madimilian, dukansu shekarunsu 12, wadanda suke nuna cewa, rayuwar Hildebrandt a matsayin uwa cike take da matakai iri-iri.

Amma haihuwar ’ya’ya a irin waɗannan shekarun na tsufa ba kowa ba ne ke samun hakan.

Henrich ya yi gargaɗin cewa, masu juna biyu a shekarun tsufa na rayuwa cikin haɗari.

Ya bayyana cewa, “matsaloli irin su hawan jini da haihuwar jariri kafin mako 37 da kuma al’amurran da suka shafi zuciya da jijiyoyin jini yawanci na karuwa da shekaru”.

Ta ce, tana ta samun sakonnin taya murna da soyayya daga abokanta da danginta bayan sanar da haihuwar Philipp.

“Na yi ta samun sakonnin fatan alheri,” in ji ta TODAY.com.

A halin da ake ciki, masana kiwon lafiya sun yi imanin cewa, ba koyaushe shekaru suke taƙaita batun haihuwa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Daruruwan ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Masallacin Kudus
  • Yadda kisan mutum fiye da 50 a Filato ya tayar da ƙura
  • Babban Daraktan Hukumar IAEA, Zai Ziyarci Iran ranar Laraba
  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa
  • ’Yar shekara 66 ta haifi ɗanta na 10 da kanta
  • Bello Turji ya kashe manoma 11 a Sakkwato
  • Shugaban Kasar Iran Ya Mika Ta’aziyyar Ta Rasuwar Wanda Ya Assasa Hukumar  Makamashin Nukiliya Ta Iran
  • ’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara
  • Newcastle Na Gab Da Samun Gurbi A Gasar Zakarun Turai
  • Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?