Amurka ta dakatar da bai wa Afirka ta Kudu tallafi
Published: 8th, February 2025 GMT
Gwamnatin Amurka ta sanar da janye tallafin da take bai wa Afirka ta Kudu yayin da alaƙa tsakanin ƙasashen biyu ta lalace a dalilin dokar karɓe gonakin fararen fata da Shugaba Cyril Ramaphosa ya amince da ita.
Shugaba Donald Trump ya ce Amurka za ta katse duk wani tallafin da take ba wa Afirka ta Kudu ciki har da na kuɗi a wani mataki na nuna adawa da dokar kwace filayen noma da Shugaba Cyril Ramaphosa na kasar ya rattabawa hannu.
Shugaba Trump ya ce Amurka ba za ta taimaka wa gwamnatin Pretoria ba, duba da yadda take ci gaba da take haƙƙin ɗan Adam, da kuma yi wa siyasar Amurka ta ƙetare karan tsaye, inda ya soki zargin Isra’ila da aikata laififukan yaƙin da Afirka ta Kudun ta yi a baya, da ma hulɗarta da Iran a wani ƙudirin da ya sakawa hannu a ranar Juma’a.
Sai dai tun a gabanin matakin na shugaban Trump ya soma aiki, a wani jawabinsa, Shugaba Cyril Ramaphosa na Afirka ta Kudun ya ce kasarsa ba za ta kawar da ido ga duk wata barazana ba.
Tun farkon wannan wata na Fabrairu ne Donald Trump ya ce zai yanke duk wasu kuɗaɗe da Amurka ke bai wa Afirka ta Kudu har sai an kammala cikakken bincike kan matakin gwamnatin ƙasar na ƙwace filaye mallakar fararen fata ba bisa ƙa’ida ba.
Barazanar na zuwa ne yayin da a ƙarshen watan Janairun da ya gabata Shugaba Ramaphosa ya ƙaddamar da dokar da ta bai wa gwamnati damar ƙwace wasu filaye galibi mallakin fararen fata ba tare da biyan diyya ba a wani mataki na samar da daidaito da kuma adalci ga ’yan kasar.
Gwamnatin Afirka ta Kudu ta bayyana matakin a matsayin wani yunƙuri na gyaran kura-kurai na rashin daidaito da ƙasar ta gada daga Turawan mulkin mallakar na Birtaniya.
Sai dai wannan mataki ya gamu da suka daga masu ra’ayin mazan jiya ciki har da attajirin nan Elon Musk ɗan asalin Afrika ta Kudu wanda ke da kusanci da shugaba Donald Trump.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: wa Afirka ta Kudu
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin da dimokuraɗiyya ta gaza kawo ci gaba a Afirka — Obasanjo
Tsohon Shugaban Nijeriya, Cif Olusegun Obasanjo ya ce mulkin dimokuraɗiyya ya gaza wajen kawo ci gaba a nahiyar Afirka.
Ya ce tsarin ya gaza ne saboda abin da ya ƙunsa bai zo daidai da al’adu, da yadda ake tafiyar da rayuwa a nahiyar ba, da abubuwan da mutanen nahiyar suka yi amanna da su ba.
Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe Kantoman Ribas ya naɗa sabon Sakataren GwamnatiTsohon shugaban na wannan furuci ne a Abuja a wurin wani taron bikin cika shekaru 60 a duniya na tsohon mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai kuma tsohon Gwamnan Imo, Emeka Ihedioha.
Obasanjo ya buga misali da yadda tsohon shugaban Amurka, Abraham Lincoln, ya bayyana tsarin dimokuraɗiyya da cewa gwamnati ce ta mutane da mutane ke jagoranta domin al’umma.
Ya ƙara da cewa tsari ne da ake yu domin kowa ya amfana, ba wai wani ɓangaren na al’umma ba ko wasu mutane ƙalilan ba.
Obasanjo ya kuma bayyana cewa kafin zuwan dimokuraɗiyyar ƙasashen yamma, Afirka na da nata tsarin shugabancin wanda ke kula da buƙatun kowa.
A cewarsa wannan tsarin shi ne dimokuraɗiyya, ba abin da ake kira dimokuraɗiyya ba a yau wanda ke bai wa shugabanni damar karɓar duk abin da suke so ba bisa ƙa’ida ba da kuma ta hanyar cin hanci da rashawa su ce wa mutane su je kotu idan suna da ja.
Obasanjo ya ce matuƙar ba a sake fasalin dimokuraɗiyya ta yi daidai da al’adu da manufofin ’yan Afirka da kuma mutunta buƙatun jama’a ba, to za ta ci gaba da durƙushewa kuma a ƙarshe ta mutu murus a nahiyar.
Daga cikin waɗanda suka halarci taron akwai tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar da tsoffin gwamnonin Anambra da Ribas —Peter Obi da Rotimi Amaechi.
Sauran mahalartan sun haɗa da tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo, tsoffin Shugabannin Majalisar Dattawa — David Mark da Ken Nnamani da tsoffin gwamnonin Sakkwato da Kuros Riba — Aminu Waziri Tambuwal da Donald Duke.