Kotun hukunta manya-manyan laifuka ta kasa da kasa ICC ta yi allawadai da takunkuman da gwamnatin Amurka ta dorawa kotun, ta kuma kara da cewa zata ci gaba da aikinta na tabbatar da adalci a duniya kamar yadda ta saba.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa kotun ICC kotu ce wacce take karban koke-koke na mutane da kasashe a duk fadin duniya, amma wacce gwamnatin Amurka ta ke son takaita ikonta don tallafawa HKI a yakin da take fafatawa da Falasdinawa wadanda ta mamaye kasarsu fiye da shekaru 76 da suka gabata.

A ranar Alhamis da ta gabata ce shugaban kasar Amurka Donal Trump ya sanya hannu a kan wata doka wacce ta dorawa kotun ta ICC takunkuman tattalin arziki masu tsanani da kuma hana jami’anta tafiye-tafiye zuwa Amurka. Shugaban ya ambaci sammacin da kotun ta fitar na kama firai ministan HKI Benyamin Natanyahu wanda ya aikata laifukan yaki a gaza, a matsayin hujjarsa ta dorawa kotun wadannan takunkuman.

Kasashe kimani 79 daga ciki har da Canada, Mexico da Najeriya sun ja hankalin kasashen duniya kan cewa wadannan takunkuman kan ICC zai sa a kara aikata laifuffukan yaki a duniya. Sanna sai wargaza dokokin kasa da kasa da dama.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran

Gwamnatin Amurka ta sanar da cewa: Ba ta neman tada tashin hankali tsakaninta da Iran

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Amurka Samuel Werberg ya bayyana cewa: Kasarsa ba ta neman kara ruruta wutar rikici da Iran, yana mai jaddada cewa har yanzu kofar diflomasiyya a bude take, duk kuwa da kakkausar murya da Amurka ta yi na kin amincewa Iran ta mallaki makamin nukiliya.

Werberg ya kara da cewa; Za su ci gaba da riko da siyasar matsin lamba da nufin dakatar da ci gaba a shirin nukiliyar Iran.

Kakakin na Amurka ya bayyana cewa, “Dole ne Iran ta nuna kyakkyawar niyyarta kafin ta yi magana kan duk wata nasara da za a samu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ina Dalilin Da Ya Sa Cinikin Shige Da Fice Na Kasar Sin Ke Samun Bunkasuwa Mai Dorewa Ba Tare Da Tangarda Ba?
  • Sin Kasuwar Duniya Ce Kuma Dama Ce Ga Kasa Da Kasa
  • Amurka, Ki Fahimci Cewa “Girma Da Arziki Ke Sa A Ja Bajimin Sa Da Zaren Abawa”
  • Kokarin Da Iran Take A Tattaunawa Da Amurka Shi Ne Dage Mata Takunkuman Zaluncin Da Aka Dora Mata
  • Sin Na Maraba Da Masu Zuba Jari Domin Su More Damammakin Bunkasarta
  • Iran Zata Yaye Labulen Ire-Iren Makamanta Na Musamman Da Ta Mallaka Domin Kare Kai
  • Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran
  • Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu
  • Dagewa Iran Takunkuman Zalunci Na Daga Cikin Manufofin Tattaunawa Da Amurka: Aref
  • Shugaban Burkina Faso Ya Yi Fatali Da Tayin Saudiyya Na Gina Masallatai 200 A Kasarsa