Mata a Karamar Hukumar Danja suna kira ga Gwamnatin Jihar Katsina da ta gyara hanyar Tsangamawa a Babban Rafi saboda yawan rasuwar mata masu juna biyu da jariransu.

 

Sun yi wannan kira ne a yayin wani taron gaggawa da manyan jiga-jigan al’umma suka shirya domin tattauna matsalar da ta dade tana addabar jama’a – hanyar Tsangamawa.

 

Hanyar Tsangamawa da ke Babban Rafi, Karamar Hukumar Danja, Jihar Katsina, ta haddasa mutuwar mata masu juna biyu da jariransu, musamman a lokacin damina.

 

Duk da yawan koke da rokon gwamnati, har yanzu ba a dauki matakin gyara hanyar ba.

 

A wata hira da suka yi da Radio Nigeria, wasu daga cikin matan yankin sun bayyana cewa mata masu juna biyu da jariransu ne suka fi fuskantar barazana, musamman a lokacin damina, saboda wahalar kai su asibiti sakamakon mummunan halin da hanyar take ciki.

 

Duk da cewa akwai cibiyar kiwon lafiya a yankin, ginin ya lalace, kuma yawancin ma’aikatan jinya da na lafiya ba sa iya zuwa aiki akai-akai saboda matsalar hanya.

 

Wata uwa mai ‘ya’ya hudu a yankin, Hajara Ibrahim, ta bayyana bakin cikinta, tana mai cewa har yanzu babu wata gwamnati da ta nuna musu tausayawa, duk da cewa suna da hakkin rayuwa mai inganci.

 

Malama Tayyiba Muktari daga Babban Rafi ta bada labarin yadda ta tsira da kyar a cikin juna biyunta na baya, inda ta ce nufin Allah ne ya sa ta tsira, sannan ta roki Gwamnatin Jihar Katsina da ta dauki matakin gaggawa kan hanyar.

 

Haka kuma, wata mata daga yankin, Fatima Abdullahi, ta koka kan yadda mummunan yanayin hanyar ke hana mazajensu fita neman abin dogaro da rayuwa.

 

Haka nan, wani tsohon jami’in lafiya a Jihar Katsina, Dr. Haruna Abubakar, ya bukaci Gwamnatin Jihar Katsina da ta saka aikin gina hanyar Tsangamawa, Babban Rafi a kasafin kudin bana saboda mahimmancinsa ga al’umma.

 

Matan yankin sun roki Gwamnan Jihar Katsina, Dr. Dikko Umar Radda, da ya tausaya musu da iyalansu ta hanyar gyara hanyar.

 

Duk da cewa hanyar tana da kimanin kilomita 23 kacal, gwamnatocin baya sun kasa gyarata. Dole ne gwamnati ta fara fifita yankunan karkara wajen bayar da kwangiloli domin inganta rayuwar al’umma.

 

Cov/Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jariransu

এছাড়াও পড়ুন:

Fadin Yankin Da Ke Fama Da Zaizayar Kasa Na Kasar Sin Ya Ragu A 2024 

Ma’aikatar kula da albarkatun ruwa ta kasar Sin ta bayyana a jiya Juma’a cewa, fadin yankin kasar dake fama da zaizayar kasa ya ragu zuwa murabba’in kilomita miliyan 2.6019 a shekarar 2024, wanda ya samu raguwar murabba’in kilomita 25,700, idan aka kwatanta da na shekarar 2023.

Wadanann alkaluman wani bangare ne na sakamakon aikin sa ido kan zaizayar kasa a kasar Sin a shekarar 2024, wanda aka kammala a kwanan nan.

Wakilin Musamman Na Xi Ya Halarci Bikin Rantsar Da Shugabar Namibiya Sin Ta Ba Da Jawabi A Kwamitin Kare Hakkin Bil’adama Na MDD A Madadin Kungiyar Abokantaka Ta Inganta Hakkin Bil’adama

Wani jami’in ma’aikatar ya bayyana cewa, sakamakon da aka samu ya nuna cewa, ana samun ci gaba bisa daidaito wajen magance zaizayar kasa a kasar Sin, inda aka samu raguwar fadin yankin da ke fuskantar matsalar da ma karfin zaizayar kasa, gami da raguwar zaizayar kasa bisa dalilan ruwa da iska.

Manyan kogunan da suka hada da kogin Yangtze, Rawayen Kogi, da kogin Huaihe, sun kai kashi 73.19 cikin 100 na yankin da aka samu raguwar zaizayar kasa a fadin kasar baki daya. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jakadan Sin A Amurka: Mayar Da Karin Haraji Makami Kaikayi Ne Da Zai Koma Kan Mashekiya
  • Gombe Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.1 Don Samar Da Fitilun Hanya Masu Aiki Da Hasken Rana
  • Mata sun ƙwace kasuwancin kayan lambu a Gombe
  • Hikimar Gwamnatin Jihar Jigawa Na Kaddamar Da Shirin Gina Rijiyoyin Burtsatsan Noman Rani
  • Fadin Yankin Da Ke Fama Da Zaizayar Kasa Na Kasar Sin Ya Ragu A 2024 
  • Za a hukunta ma’auratan da suka ci zarafin yarinya a kan mangwaro — Zulum
  • Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho
  • Sallah: Tinubu Ya Raba Wa ’Yan APC Buhun Shinkafa 7,000 A Zamfara
  • Sojoji sun ceto mutum 84 da ’yan bindiga suka sace a Katsina
  • MAGGI: Girke-girken Ramadan masu kawo sauyi da zumunta