Lalacewar Hanya Na Janyo Yawan Mutuwar Mata Masu Juna Biyu Da Jariransu A Katsina
Published: 8th, February 2025 GMT
Mata a Karamar Hukumar Danja suna kira ga Gwamnatin Jihar Katsina da ta gyara hanyar Tsangamawa a Babban Rafi saboda yawan rasuwar mata masu juna biyu da jariransu.
Sun yi wannan kira ne a yayin wani taron gaggawa da manyan jiga-jigan al’umma suka shirya domin tattauna matsalar da ta dade tana addabar jama’a – hanyar Tsangamawa.
Hanyar Tsangamawa da ke Babban Rafi, Karamar Hukumar Danja, Jihar Katsina, ta haddasa mutuwar mata masu juna biyu da jariransu, musamman a lokacin damina.
Duk da yawan koke da rokon gwamnati, har yanzu ba a dauki matakin gyara hanyar ba.
A wata hira da suka yi da Radio Nigeria, wasu daga cikin matan yankin sun bayyana cewa mata masu juna biyu da jariransu ne suka fi fuskantar barazana, musamman a lokacin damina, saboda wahalar kai su asibiti sakamakon mummunan halin da hanyar take ciki.
Duk da cewa akwai cibiyar kiwon lafiya a yankin, ginin ya lalace, kuma yawancin ma’aikatan jinya da na lafiya ba sa iya zuwa aiki akai-akai saboda matsalar hanya.
Wata uwa mai ‘ya’ya hudu a yankin, Hajara Ibrahim, ta bayyana bakin cikinta, tana mai cewa har yanzu babu wata gwamnati da ta nuna musu tausayawa, duk da cewa suna da hakkin rayuwa mai inganci.
Malama Tayyiba Muktari daga Babban Rafi ta bada labarin yadda ta tsira da kyar a cikin juna biyunta na baya, inda ta ce nufin Allah ne ya sa ta tsira, sannan ta roki Gwamnatin Jihar Katsina da ta dauki matakin gaggawa kan hanyar.
Haka kuma, wata mata daga yankin, Fatima Abdullahi, ta koka kan yadda mummunan yanayin hanyar ke hana mazajensu fita neman abin dogaro da rayuwa.
Haka nan, wani tsohon jami’in lafiya a Jihar Katsina, Dr. Haruna Abubakar, ya bukaci Gwamnatin Jihar Katsina da ta saka aikin gina hanyar Tsangamawa, Babban Rafi a kasafin kudin bana saboda mahimmancinsa ga al’umma.
Matan yankin sun roki Gwamnan Jihar Katsina, Dr. Dikko Umar Radda, da ya tausaya musu da iyalansu ta hanyar gyara hanyar.
Duk da cewa hanyar tana da kimanin kilomita 23 kacal, gwamnatocin baya sun kasa gyarata. Dole ne gwamnati ta fara fifita yankunan karkara wajen bayar da kwangiloli domin inganta rayuwar al’umma.
Cov/Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jariransu
এছাড়াও পড়ুন:
An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo
Jami’an tsaron Jihar Edo sun sake kama wasu mafarauta hudu daga Kano, makonni kadan bayan kisan gilla da ’yan bangar Jihar Edo suka yi wa ayarin wasu mafarauta 16 daga jihar Kano a jihar.
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Edo, ta ce mafarautan da aka kama sun fito ne daga Karamar Hukumar Doguwa ta Jihar Kano, kuma suna dauke da bindigogin toka guda uku, da adduna da wukake a lokacin da aka kama su.
Kakakin ’yan sanda an jihar, CSP Moses Yamu, ya ce kanawan da aka kama mafarauta ne ba kamar yadda ake yadawa a kafofin sada zumunta cewa makiyaya ba ne.
Ya bayyana cewa jami’an kungiyar tsaro ta Jhar Edo ne suka kama mafarautan sannan suka damka su ga ’yan sanda inda ake yi musu tambayoyi a ofishin ’yan sanda da ke yankin Ikpoba Hill.
’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken TinubuYa ce an, “An kama mafarautan da suka fito daga Karamar Hukumar Doguwa ta Jihar Kano a yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa yankin Uvbe da ke Karamar Hukumar Orhionwon a Jihar Edo. A halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike.”
Da haka Kwamishinan ’yan sandan jihar, Monday Agbonika, ya gargadi jama’ar jihar da su guji yada abin da ba gaskiya ba ne game da lamarin, domin yana iya tayar da zaune tsaye.
Idan ba a manta ba, a cikin watan Ramadan, gab Sallah Karama ne ’yan banga suka yi wa wasu mafarauta 16 daga Jihar Kano da ke hanyarsu ta komawa gida hutun sallah kisan gilla a yankin Uromi da ke jihar, lamarin da ya haifar da tayar da jijiyoyin wuya, inda har yanzu ake kokarin shawo kansa.