Jihar Adamawa ta rasa shahararre kuma babban malamin addinin musilunci, Sheikh Ibrahim Abubakar Daware, ranar Juma’a, bayan fama da rashin lafiya.

Sheikh Daware ya kasance malami mai karamci wanda yake koyar da darussan addini da kuma gudummawa a kasashen musulmi daban-daban da sassan jihohin Nijeriya da dama.

Dauda Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Almajirai 17 Da Suka Rasu A Sakamakon Tashin Gobara A Zamfara Uwargidan Tinubu Ta Kai Wa Gwamnan Jigawa Ziyarar Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifiyarsa Da Ɗansa

An gudanar da jana’izar malamin kamar yadda addinin musilunci ya tanada a gidansa da ke karamar hukumar Fufore a ranar Asabar.

Sheikh Ibrahim Daware, ya rasu ya na da shekaru 71, ya bar matan aure hudu da ‘ya’ya 43 da jikoki 53.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Adamawa Rasuwa Sheikh Ibrahim Abubakar Daware

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kwato Motoci 7 Da Aka Sace Da Taimakon Na’urar e-CMR A Kano

Ya ce, motocin da aka kwato sun hada da wata farar mota kirar Howo, wacce aka sace daga Riruwai, karamar hukumar Doguwa, Kano, a ranar 17 ga watan Janairu, 2025, aka kuma gano ta a Lokoja, jihar Kogi.

 

Akwai wata bakar mota kirar Honda Accord 2013, wacce aka sace daga Abuja ranar 18 ga watan Janairu, 2025, aka gano ta a filin jirgin sama na Kano.

 

Bugu da kari, akwai wata farar mota kirar Mercedes Benz GLK wacce aka sace a hanyar Magwan Kano a ranar 27 ga watan Janairu, 2025, aka gano ta a Hotoro Quarters Kano da wata jar Toyota Corolla LE da aka sace a Abuja a ranar 30 ga Janairu, 2025, aka gano ta a Kano.

 

Daya kuma wata bakar mota kirar Toyota Camry, wacce aka sace a Kaduna ranar 27 ga watan Janairu, 2025, aka gano ta a Kano.

 

Akwai Wata farar Toyota Hilux da aka sace daga Katsina a ranar 15 ga Fabrairu, 2025, aka same ta a Ring Road Bypass, Kano.

 

Har ila yau, akwai wata bakar mota ash mai suna Pontiac Vibe, wacce aka sace daga Katsina a ranar 15 ga Fabrairu, 2025, kuma aka gano ta a Ring Road Bypass, Kano.

 

Rundunar ‘yansandan ta jaddada mahimmancin rajistar motoci a na’urar e-CMR wajen bin diddigin motocin da aka sace, inda ta bukaci masu abin hawa da su yi rajista ta shafin https://cmris.npf.gov.ng don inganta tsaro.

 

Rundunar ta kuma ja hankalin jama’a da su kasance cikin taka-tsan-tsan tare da bayar da rahoton duk wani abu da suka shakku akai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jihar Kano Ta Samar Da Wani Salo Na Bunkasa Ilmin Addinin Musulunci A Jihar
  • ‘Yansanda Sun Kwato Motoci 7 Da Aka Sace Da Taimakon Na’urar e-CMR A Kano
  • Ɗaliba ta rasu yayin da gini ya rufta a GGTC Potiskum
  • An rufe Jami’ar Kogi saboda zanga-zangar ɗalibai
  • Wang Yi Ya Bayyana Ra’ayin Sin Kan Yadda Za A Karfafa Huldar Cude-Ni-In-Cude-Ka A Duniya
  • Zargin Daukar Nauyin Boko Haram: Tinubu Na Ganawar Sirri Da Akpabio A Villa
  • Amurka Ba Ta Sauya Ba Ko Kadan
  • Mutum 10 sun rasu, an lalata dukiyar N11bn yayin zanga-zangar yunwa a Kano — Rahoto
  • Gubar harsashi ta jikkata mutane dama a Zamfara
  • Daga Munich Zuwa Addis Ababa, Ci Gaban Kasashe Daban Daban Na Tabbata