Xi Jinping: Ya Kamata A Sa Kaimi Ga Aiwatar Da Shirin Farfado Da Arewa Maso Gabashin Sin A Dukkan Fannoni A Sabon Zamani
Published: 9th, February 2025 GMT
A yau Asabar, 8 ga wannan wata da safe, babban sakataren kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta Sin kuma shugaban kasar Sin Xi Jinping ya saurari rahoton aiki na kwamitin JKS da gwamnatin lardin Jilin a birnin Changchun dake lardin Jilin. Bayan kammala sauraro, shugaba Xi ya yi jawabi inda ya jaddada cewa, ya kamata hukumomin lardin Jilin su aiwatar da shirin farfado da yankin arewa maso gabashin kasar Sin a dukkan fannoni a sabon zamani da kwamitin tsakiya na JKS ya tsara, da tabbatar da tsaron kasar a fannoni 5, da maida hankali ga aikin samun ci gaba mai inganci, da bin tsarin tunanin sabon ci gaba, da bude kofa ga kasashen waje, da yin kwaskwarima a dukkan fannoni, da amfani da dama, tare da kara kokarin kirkire-kirkire don ba da gudummawa ga samun nasarar zamanantarwa irin ta kasar Sin.
Shugaba Xi ya yi nuni da cewa, samun ci gaba mai inganci yana da nasaba da yin kirkire-kirkire da tabbatar da bunkasar sauran sha’anoni. Don haka, ya kamata a ci gaba da raya tattalin arziki da kyautata tsarin raya sana’o’in gargajiya da na zamani, inda ta hakan za a kafa tsarin sana’o’in zamani mai salon musamman na lardin Jilin. (Zainab Zhang)
কীওয়ার্ড: lardin Jilin
এছাড়াও পড়ুন:
Sabon Shugaban Kasar Gabon Ya Bayyana Shiransa Na Kawo Sauyi Mai Kyau A kasar
Bayan da hukumar zaben kasar Gabon ta tabbatar da nasarar da Brice Oligui yayi a zaben shugaban kasa na karshen makon da ya gabata, shugaban ya gabatar da jawabinsa na farko ga mutanen kasar, inda ya bayyana masu kan cewa, babu jin dadi sai tare da wahala.
Shafin tanar gizo na labarai ‘Africa News” ya nakalto shugaban yana cewa muhimman al-amuran da zai sa a gaban a shugabancin kasar sun hada da sauya tsarin tattalin arzikin kasar daga dogaro da man fetur zuwa harkokin kasuwanci, har’ila yau zai yaki cin hanci da rashawa.
Brice ya ce, ya zo ne a matsayin mai gina kasa, kuma yana son taimakon su don samun nasara a wannan gagarum,in aikin.
A ranar lahadin da ta gabata ce hukumar zaben kasar Gabaon ta bada sakamakon zaben shugaban kasa wanda aka gudanar a ranar Asabar wanda ya nuna cewa masu zabe a kasar sun zabi Brice a matsayin shugaban kasa tare da samun kasha 90.4% na yawan kuri’un da aka kada, kuma yawan mutanen da suka fito kara kuri’un ya kai kasha 74%.