Aminiya:
2025-04-13@11:06:06 GMT

Ta kashe saurayinta saboda ya gaisa da tsohuwar abokiyar karatunsa

Published: 9th, February 2025 GMT

Wani matashi ɗan kasar Argentina mai shekara 23 ya rasa ransa a sakamakon daɓa masa wuƙa da budurwarsa ta yi saboda kawai ya gaisa da wata mata a kan titi.

Kishi madaidaici zai iya zama abu mai masu alaka da juna, amma mafi yawanci na iya wuce kima!

Abba ya naɗa sabon Sakataren Gwamnatin Kano Shigo da hatsi daga ƙetare ya karya farashinsa a Neja

Idan aka dubi labarin Mariano Grinspun, ɗan shekara 23 daga González Catán, wani birni a lardin Buenos Aires na Argentina, wanda budurwarsa mai tsananin kishi ta caka masa wuka wanda ya yi sanadiyya mutuwarsa bayan ya gaisa da wata tsohuwar abokiyar karatunsa a titi, za a ga abin akwai ban mamaki.

Abin ya faru ne ranar 21 ga Oktoba 2024, kusa da titin Balboa da La Bastilla, a birnin González Catan.

Mariano da budurwarsa Natacha Palavecino, suna tafiya tare, sai suka ci karo da wata mata da ta gaida Mariano kuma ta tambaye shi halin da yake ciki.

Gaisuwar ta haukata budurwar Mariano, inda ta zaro wuƙa a ɓoye ta afka masa.

Matar da ta gaisa da Mariano Grinspun, tsohuwar abokiyar karatunsa ce, amma hakan ya tunzura budurwarsa.

Natacha ta kai hannu ta ɗauki wata boyayyiyar wuƙa sannan ta yanki matar mai suna LC kamar yadda kafafen yada labarai na kasar Argentina suka bayyana.

Bayan yankar LC da wuƙar ta faɗi kasa ta yi yunƙurin ƙara yankar ta, amma ta sa hannunta ta kare, wanda da watakila ta kashe ta da ba don wani mutumin ba wanda ya yi nasarar daƙile faruwar hakan.

Abin takaici, Mariano Grinspun bai yi sa’a sosai ba, domin bayan da ta gaza kashe matar, Natacha Palavecino ta far wa saurayin nata, inda ta daɓa masa wuƙa a kirji.

Masoyan sun yi ta muhawara ta tsawon mintuna da dama, kamar yadda kyamarorin sa ido na CCTV a yankin suka nuna, wanda a lokacin Mariano ya fadi kasa yana shure-shure.

Zuwa wani lokaci, ya kasa tashi sai budurwarsa mai shekara 32 ta kai masa hari da hannunta.

Shaidun gani da ido sun kira jami’an agajin gaggawa, amma ba su iya yin komai ba wajen ceto rayuwarsa.

Wani bincike da aka gudanar ya bayyana tarihin tashin hankali Natacha Palavecino.

A 2021, an yanke mata hukuncin daurin shekara daya a gidan yari saboda ta dava wa wani tsohon saurayinta wuƙa a kirji, har ma Mariano da kansa ya kai ƙarar ta ga ’yan sanda saboda barazanar da ta yi masa da kuma yi masa rauni a jiki.

A watan Yulin shekarar bara ce aka ba da umarnin hana Natacha duk wata alaka da Mariano.

Sai dai bayan wucewar wa’adin, sai ya yanke shawarar sake dawowa da alakar.

Palavecino mai shekaru 32 za ta iya kasancewa a gidan yari tsawon shekaru saboda wannan laifi na kisan saurayinta da kuma yunkurin kisan matar da ta gaishe shi a kan titi.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Argentina

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen Filato

Rahotanni sun ce an kashe wani uba da ‘ya’yansa biyu a ƙauyen Zogu da ke Gundumar Miango a Ƙaramar hukumar Bassa ta jihar Filato.

Kakakin Ƙungiyar ci gaban Irigwe (IDA), Sam Jugo, wanda ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin a Jos, ya bayyana sunayen waɗanda harin ya rutsa da su kamar haka, Weyi Gebeh a mai shekara 56, da Zhu Weyi mai shekara 25 da Henry Weyi mai shekara 16.

‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano

A cewar Jugo, an kashe mutanen ne cikin dare a lokacin da suke barci, inda ya bayyana lamarin a matsayin dabbanci.

Ya ce, “An sanar da shugabannin Ƙungiyar ci gaban Irigwe (IDA) game da wani harin da aka kai ƙauyen Zogu, Miango wanda ya yi sanadin mutuwar wani uba da ‘ya’yansa biyu waɗanda suka haɗa da: Weyi Gebeh da Zhu Weyi da Henry Weyi.

“Wannan harin na baya-bayan nan ya kai ga mutuwar mutane tara a cikin makon nan kaɗai, Ƙungiyar IDA ta nuna rashin jin daɗinta game da taɓarɓarewar al’amura a yankin Irigwe tare da yin kira ga jami’an tsaro da su yi duk abin da ya kamata don daƙile wannan ɓarna a yankinmu tare da kama waɗanda suka aikata laifin don fuskantar shari’a.

Kakakin rundunar ‘Operation Safe Haven’ Manjo Samson Zhakom da rundunar ’yan sandan jihar, DSP Alabo Alfred, har yanzu ba su mayar da martani ga saƙon da wakilinmu ya aika masu ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ta kai ƙarar kamfanin jirgi da fasinja kan kukan yaro
  • Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno
  • An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen Filato
  • Kallo Daya Mutum Za Yi Min Ya Gane Masana’antar Kannywood Ta Canza Rayuwata -Farida Abdullahi
  • An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Gwaska da mayaƙa 100 a Katsina
  •  Limamin Tehran: Iran Ba Ta Tsoron Tattaunawa
  • Mutane Da Yawa Sun Jikkata Bayan Fashewar Bam A Wata Kasuwa A Ikeja
  • NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassa Al-Mujtaba (a) 107
  • Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto