An Yi Bikin Cika Shekaru 46 Da Samun Nasarar Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran A Nijar
Published: 9th, February 2025 GMT
A Nijar an yi bikin cika shekaru 46 da samun nasarar juyin juya halin Musulunci a Iran a Yamai babban birnin kasar, bikin da ya samu halartar ‘yan siyasa da jakadu da jami’an diflomasiyya da ‘yan jarida.
Manyan baki da suka halarci bikin sun hada da ministan harkokin wajen Nijar, magajin garin Yamai da kuma wakili na musamman na Firaministan Nijar.
A yayin wannan biki, jakadan Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Nijar Ali Tiztak ya gabatar da jawabi, inda ya yi ishara da irin nasarorin da Tehran ta samu cikin shekaru arba’in da suka gabata.
Ali Tiztak ya ci gaba da cewa, duk da takunkumin zalinci da kalubalen da Jamhuriyar Musulunci ta Iran take fuskanta tun ranar farko bayan nasarar juyin juya halin Musulunci, ta samu ci gaba da dama a fannonin kiwon lafiya da jiyya, ilimi, kimiyya da fasaha, hakkin dan Adam, tsaro da tsaro.
A wani bangare na jawabin nasa, ya yi ishara da muhimman batutuwan da suka shafi manufofin ketare na kasar Iran, wato tabbatar da moriyar kasar, kiyaye tsaron kasa, tabbatar da daidaiton alaka da dukkanin al’ummomi bisa tushen tattaunawa, daidaito da mutunta juna, raya diflomasiyya da tattalin arziki da kuma mutunta ‘yancin kai da yankunan kasashen.
Yayin da yake ishara da alakar da ke tsakanin Tehran da Yamai, jakadan Iran a Jamhuriyar Nijar ya bayyana aniyar manyan jami’an kasashen biyu na fadada hadin gwiwarsu a fannonin siyasa, tattalin arziki, al’adu da kuma jin kai.
Bugu da kari, Ali Tiztak ya yaba da kokarin gwamnati da al’ummar Nijar a cikin shekara daya da rabi na tabbatar da ‘yancin kansu, ta fuskar tattalin arziki, tsaro da zaman lafiyar al’umma.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Rohoton Kwamitin Kare Hakkin Dan Adam Ya Tabbatar Da Tafka Manyan Laifukan Cin Zarafin Bil-Adama A Siriya
Wani rahoton kare hakkin bil adama ya tabbatar da aikata manyan laifuka a gabar tekun Siriya tare da yin kira da a kare fararen hula
Kwamitin da ke bin diddigin kare hakkin bil adama a kasar Siriya karkashin jagorancin dan gwagwarmaya Haitham Al-Manna, ya fitar da wani cikakken rahoton take hakkin dan Adam mai shafuka 72 da ke kunshe da jerin munanan laifukan da aka yi wa fararen hula a gabar tekun Siriya, yana mai bayyana shi a matsayin “neman shafe wata al’ummar daga kan doron kasa a kan tubalin sabanin Mazhaba”.
Rahoton wanda masu fafutuka 12 suka shirya, ya zo ne bayan kisan kiyashin da aka fara a ranar 6 ga Maris.
Rahoton ya yi nuni da wani tsari na cin zarafi da ake yi wa fararen hula, da suka hada da kashe-kashen gilla, azabtarwa, tilasta yin gudun hijira, da wawure dukiyoyi. Har ila yau, rahoton ya yi nuni da yadda dakarun gwamnati da kungiyoyin masu dauke da makamai suka shiga cikin wadannan laifuka, da kuma dogaro da shaidar iyalan wadanda abin ya shafa na tattara bayanan da aka hana binne mutane da kuma wulakanta fararen hula.