Shugabannin kungiyoyin raya kasashen gabashi da kuma kusanci na Afrika (EAC da SADC), sun yi kira da a gaggauta tsagaita wuta a gabashin Jamhuriyar DR Congo.

Bangarorin sun bayyana hakan a wani taron hadin guiwa da suka gudanar a birnin Dar es Salaam, na kasar Tanzania a jiya Asabar.

A cikin wata sanarwar hadin gwiwa da suka fitar, sun kuma bukaci da bude manyan tituna da filin jirgin saman Goma, da kuma tattaunawa kai tsaye tsakanin Kinshasa da kungiyar M23.

Saidai taron, bai yi Allah wadai da Rwanda ba kan shigar ta cikin rikicin ba.

Taron na hadin gwiwa ya tabbatar da hadin kai da jajircewa wajen ci gaba da marawa DRC baya a kokarin da take yi na kare ‘yancin kanta, da ikonta da kuma yankunanta,” a cewar sanarwar karshen taron.

A nata bangaren, tawagar ta Rwanda ta yi imanin cewa, wannan taro ya cika burin Kigali.

Wanda ya bada dama don dawo da zaman lafiya a gabashin DRC”, a cewar ministan harkokin wajen kasar a shafinsa na X.

“Taron na hadin gwiwa ya bukaci shugabannin rundunar tsaro ta AEC (Al’ummar Gabashin Afirka) da SADC (Al’ummar Gabashin Afirka ta Kudu) da su gana cikin kwanaki biyar don fidda hanyoyin tsagaita wuta ba tare da wani sharadi ba da kuma dakatar da fada.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An rantsar da shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Katsina

A wannan Litinin ɗin ce ne aka rantsar da sabbin shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Jihar Katsina waɗanda aka gudanar da zaɓensu a ranar 15 ga watan Fabrairu, 2025.

Babban Jojin Jihar Katsina, Mai Shari’a Musa Danladi Abubakar ne ya jagoranci rantsar da sabbin shugabannin ƙananan hukumomin.

’Yar shekara 66 ta haifi ɗanta na 10 da kanta Bello Turji ya kashe manoma 11 a Sakkwato

Sai dai gab da lokacin da za a rantsar da su, ɗaya daga cikinsu ya faɗi ya sume a lokacin da yake ƙoƙarin shiga rumfar da aka tanadar masu.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Bakori Honarabil Aminu Ɗan Hamidu shi ne wanda ya faɗi kuma aka ɗauka ranga-ranga zuwa asibiti.

Binciken da muka yi ya nuna cewa, shugaban ya take wani sashe na babbar rigar shi ne ba tare da ya yi la’akari ba yayin da ya yunƙura da ƙarfi don hawa matattakalar shiga rumfar, lamarin da ya janyo rigar ta shaƙe shi ya faɗi a sume.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsangayar Ilimi Ta BUK Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa
  • Iran, Iraki Sun Karfafa Dangantakar Makamashi
  • An rantsar da shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Katsina
  •  Tsoffin Ma’aikatan Hukumar Leken Asiri HKI  Mosad Sun Shiga Cikin Masu Kiran A Kawo Karshen Yaki Da Gaza
  • Xi Da Prabowo Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Sin Da Indonesiya
  • NATE Ta Rantsarda Sabbin Shugabanni Reshen Jihar Kaduna
  • Inganta Rayuwar Al’umma: Amurka Da Ƙungiyar Kasuwanci Ta Nijeriya Sun Karrama Gwamna Lawal
  • Sin Da Sifaniya Sun Daga Matsayin Hadin Gwiwa A Fannin Shirya Fina-finai
  • Saudiya Tace Shigo Da Agaji Cikin Gaza Bai Da Dangantaka Da Tsagaita Wuta
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro