Shugabannin kungiyoyin raya kasashen gabashi da kuma kusanci na Afrika (EAC da SADC), sun yi kira da a gaggauta tsagaita wuta a gabashin Jamhuriyar DR Congo.

Bangarorin sun bayyana hakan a wani taron hadin guiwa da suka gudanar a birnin Dar es Salaam, na kasar Tanzania a jiya Asabar.

A cikin wata sanarwar hadin gwiwa da suka fitar, sun kuma bukaci da bude manyan tituna da filin jirgin saman Goma, da kuma tattaunawa kai tsaye tsakanin Kinshasa da kungiyar M23.

Saidai taron, bai yi Allah wadai da Rwanda ba kan shigar ta cikin rikicin ba.

Taron na hadin gwiwa ya tabbatar da hadin kai da jajircewa wajen ci gaba da marawa DRC baya a kokarin da take yi na kare ‘yancin kanta, da ikonta da kuma yankunanta,” a cewar sanarwar karshen taron.

A nata bangaren, tawagar ta Rwanda ta yi imanin cewa, wannan taro ya cika burin Kigali.

Wanda ya bada dama don dawo da zaman lafiya a gabashin DRC”, a cewar ministan harkokin wajen kasar a shafinsa na X.

“Taron na hadin gwiwa ya bukaci shugabannin rundunar tsaro ta AEC (Al’ummar Gabashin Afirka) da SADC (Al’ummar Gabashin Afirka ta Kudu) da su gana cikin kwanaki biyar don fidda hanyoyin tsagaita wuta ba tare da wani sharadi ba da kuma dakatar da fada.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas Za Ta Saki Dukkan Fursunonin Isra’ila Da Ke Hannunta

Hamas ta nuna shirin ta na sakin duk sauran fursunonin da take riƙe da su Gaza a cikin musanye guda cikin mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta tsakaninnta da Isra’ila.

Babban Jami’in Hamas, Taher al-Nunu, ne ya bayyanawa masu shiga tsakani cewa ƙungiyar tana da niyyar sakin fursunonin gaba ɗaya maimakon rarraba su kashi-kashi kamar yadda aka yi a mataki na farko, wanda ya ce tabbaci ne da kuma shirinsu na ci gaba da warware batun.

Isra’ila Ta Fara Sakin Fursunonin Falasɗinawa 369, Ciki Har Da Waɗanda Aka Yanke Wa Hukuncin Ɗaurin Rai Da Rai Hamas Ta Amince Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Isra’ila

A ƙarƙashin yarjejeniyar tsagaita wutar na yanzu, an saki fursunonin Isra’ila 19 a madadin fiye da Falasdinawa 1,100 da ke gidajen yari, wanda a yanzu fursunoni 58 ne za su rage a Gaza, sannan ana shirin mayar da gawarwakin fursunoni takwas da suka mutu cikin matakai biyu.

Ana sa ran mataki na biyu na yarjejeniyar zai fayyace matakan da za a ɗauka domin cimma cikakken tsagaita wuta, inda ake shirin fara tattaunawa a wannan mako.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DRC : Kwamitin Tsaro Na MDD, Ya Yi Da Goyan Bayan Da Rwanda Ke Bai Wa ‘Yan Tawayen M23
  • Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Taimakawa Shirye-shiryen Zabe A Jamhuriyar Afrika Ta Tsakiya
  • Wasu sassan Abuja za su kasance cikin duhu a ƙarshen mako – TCN
  • Limamin  Juma’a Na Tehran Ya Jaddada Muhimmancin Hadin Kai A Tsakanin Al’ummar Musulmi
  • MDD Ta Yi Gargadin Barkewar Yakin Da Zai Hada Kasashe A DRC
  • Jami’an Diblomasiyya Daga Kungiyar G20 Da Dama Sun Isa Afrika Ta Kudu
  • Hamas Za Ta Saki Dukkan Fursunonin Isra’ila Da Ke Hannunta
  • Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Da Sarkin Kasar Qatar Kan Muhimmancin Hadin Gwiwa Da Taimakekkeniya Tsakaninsu
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Watsi Da Karin Shuruddan Gwamnatin ‘Yan Sayoniyya Kan Tsagaita Bude Wuta
  • An Rantsar Da Sabbin Shugabannin Kungiyar Manyan Sakatarorin Jihar Zamfara