Iran Ta Ce A Shirye Take Ta Tallafa Wa Burkina Faso A Yaki Da Ta’addanci
Published: 9th, February 2025 GMT
Iran ta ce a shirye take ta tallafa wa Burkina faso a yakin da take da ta’addanci.
Wannan bayyanin ya foto ne bayan wata ganawa tsakanin Firaministan Burkina Faso Rimtalba Jean Emmanuel Ouédraogo da jakadan Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Burkina Faso, Mista Mojtaba Faghihi a Ouagadougou.
Taron dai ya baiwa mutanen biyu damar sake yin nazari kan hadin gwiwar dake tsakanin kasashensu.
A cikin wannan yanayi, Iran ta bayyana aniyar ta na tallafawa Burkina Faso, a kokarinta na dakile matsalar rashin tsaro.
Tehran, ta bakin jakadanta, ta kuma bayyana sha’awarta kan sauran fannonin hadin gwiwa, kamar su noma, masana’antu, likitanci da al’adu.
Ya ce Iran a shirye take ta ba da dukkan goyon bayan da ya dace ga Burkina Faso, yana mai jaddada a shirye Tehran ta ke na mara wa Ouagadougou baya a yakin da take yi da ta’addanci.
Wannan furuci na zuwa ne a wani yanayi da Burkina Faso ke fuskantar matsalar rashin tsaro, tana neman karkata dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare.
Firaministan Burkina Faso ya yi marhabin da wannan shiri, yana mai jaddada matsayin kasarsa da kokarin Iran wajen yaki da ta’addanci.
Ya kuma bayyana goyon bayansa ga fadada hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu. Wannan taron ya ba da damar tattaunawa kan yadda za a yi hadin gwiwa a bangarori da dama da suka hada da noma, masana’antu, likitanci da al’adu, wanda ke nuna muradin karfafa alaka tsakanin kasashen biyu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Aljeriya ta yi barazanar korar jami’an diflomasiyyar Faransa 12
Rikicin diflomasiyya tsakanin Paris da Algiers na dada kamari, inda Aljeriya ta bukaci wasu jami’an diflomasiyyar Faransa 12 da su fice daga kasar cikin sa’o’i 48.
Ministan harkokin wajen Faransa Jean-Noël Barrot ya sanar cewa, Aljeriya ta bukaci jami’an diflomasiyyar Faransa da su fice daga kasar bayan kama wasu ‘yan kasar Aljeriya uku a Faransa.
“Ina kira ga hukumomin Aljeriya da su yi watsi da wannan matakin, inda ya kara da cewa: “Idan har aka ci gaba da yanke shawarar korar wakilanmu, ba mu da wani zabi illa mu mayar da martani cikin gaggawa.”
Shekaru da dama, alakar diflomatoyyar da ke tsakanin Aljeriya da Faransa ta yi tsami.
A farkon watan Afrilu, ministan harkokin wajen Faransa ya je kasar Aljeriya, domin kokarin warware matsalolin da suka jefa kasashen biyu cikin tabarbarewar diflomasiyya.
Bayan ganawa da shugaban kasar Aljeriya, Abdelmadjid Tebboune, Jean-Noël Barrot ya bayyana muradin kasashen biyu na “sake gina dangantakar abokantaka.”
A daidai lokacin da ake fuskantar tsamin dangantaka tsakanin Algiers da Paris, ofishin mai gabatar da kara na Faransa ya tuhumi, wasu ‘yan kasar Aljeriya uku, a ranar 11 ga Afrilu, ciki har da wani jami’in ofishin jakadanci, da zarginsu da hannu a sace wani dan adawar gwamnatin Algeria, Amir Boukhors, da aka sani da “AmirDZ na Paris” a cikin 2024.
Aljeriya ta yi kakkausar suka a ranar Asabar, 12 ga Afrilu, don nuna adawa da kamawa da tsare daya daga cikin jami’an ofishin jakadancinta a kasar Faransa tare da neman a gaggauta sakin shi.