HausaTv:
2025-04-14@17:18:49 GMT

Iran Ta Kira Taron Gaggawa Na Ministocin OIC, Kan Shirin Trump Na Kwace Gaza

Published: 9th, February 2025 GMT

Iran ta bukaci taron gaggawa na ministocin harkokin wajen kasashen kungiyar hadin kan kasashen Musulmi ta OIC, game da shirin shugaba Donald Trump na Amurka na kwace Gaza da kuma korar al’ummar Zirin.

Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran, yana mai jaddada cewa haramtaccen shirin” na shugaban kasar Amurka kan Gaza ya gamu da kakkausan ra’ayi daga kasashe daban-daban, inda ya yi kira da a gudanar da taron gaggawa na ministocin kungiyar ta OIC domin tattaunawa da yanke shawara kan wannan batu.

A wata tattaunawa daban daban ta wayar tarho da wasu takwarorinsa a yammacin jiya Asabar ministan harkokin wajen na Iran Sayyid Abbas Araghchi da takwaransa na kasar Masar Badr Abdel-Aty, Abbas Araghchi ya yi Allah wadai da shirin hadin gwiwa tsakanin Amurka da Isra’ila na tilastawa mutanen Gaza gudun hijira a yankin da aka yi wa kawanya.

Mista Araghchi ya ce dole ne dukkan al’ummar musulmi su tashi tsaye wajen dakile wannan makirci.

Araghchi yakuma tattauna da babban sakataren kungiyar hadin kan kasashen musulmi OIC Hussein Ibrahim Taha ta wayar tarho.

Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya yi kira da a gudanar da wani taro na musamman na kungiyar domin daukar kwararan matakai masu inganci na kare hakkin Falasdinawa.

Ya kuma bayyana babban nauyin da ke wuyan kasashen musulmi na tallafawa Falasdinawa da ake zalunta, musamman hakkinsu na cin gashin kansu.

“Shirin tilastawa Falasdinawa kaura daga Gaza ba wa kawai babban laifi ba ne da ke da alaka da ‘kisan kare dangi,’ barazana ne ga tsaron yankin da kuma duniya baki daya,” in ji shi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya Ta Jaddada Aniyar Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing

 

Kazalika, mahalarta taron sun jaddada muhimmancin inganta samar da ayyukan yi, da karfafa tattalin arziki, da kyautata zaman rayuwar ’yan Najeriya, ta hanyar kulla huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare da kasar Sin. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Tsoffin Ma’aikatan Hukumar Leken Asiri HKI  Mosad Sun Shiga Cikin Masu Kiran A Kawo Karshen Yaki Da Gaza
  • Gaza: Mutane 38 Sun Yi Shahada A Yau Litinin
  • Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Sun Yi Fatan Al-Khairi Ga Iran Da Amurka A Tattaunawar Shirin Nukliyar Kasar
  • Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya godewa ministan harkokin wajen kasar Omman
  • Ukraine na Fuskantar Wata Barazana, Dangane Da Bukatar Amurka Na Kwace Iko Da Cibiyar Gas Na Rasha  A cikin Kasar
  • Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Amurka da Iran
  • Iran da Amurka zasu ci gaba da tattaunawa a mako mai zuwa
  •  A Yau Asabar Ne Ake Bude Tattaunawa A Kasar Oman Akan Shirin Makamashin Nukiliyar Iran
  • MDD: Mafi Yawancin Wadanda Yaki Ya Ci A Gaza Mata Ne Da Kananan Yara
  • Najeriya Ta Jaddada Aniyar Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing