Aminiya:
2025-04-14@18:31:46 GMT

Me ya sa ake musayar yawu tsakanin APC da PDP?

Published: 9th, February 2025 GMT

Duk da cewa akwai sauran lokaci kafin babban zaben 2027, ana ci gaba da musayar yawu kan shirye-shiryen manyan ‘yan siyasa da ke hamayya da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu, inda suke tarurruka tare da tuntuɓar juna kan yadda za su kayar da Jam’iyyar APC mai mulki a Zaɓen 2027.

Fadar Shugaban kasa ta mayar da martani kan kalaman da wasu daga cikin ‘ya’yan jam’iyyun adawa da na cikin gidanta suke yi, inda suka zarge ta da sauka daga kan turbar da jam’iyyar take.

Katsina ta zama cibiyar haɗin kan ƙabilun ƙasa a Arewa — Gwamna Radda Ta kashe saurayinta saboda ya gaisa da tsohuwar abokiyar karatunsa

Fadar Shugaban kasa na mayar da martani ne bayan wani taro da jagororin hamayya da wasu daga cikin ‘yan Jam’iyyar APC da ke adawa da gwamnatin suka gudanar a Abuja.

Jam’iyyar ta APC dai ta ce hakan ba komai ba ne illa yunƙurin da masu adawa da gwamnatin ta Bola Ahmed Tinubu ke yi na kawar da hankalin Tinubu daga hidimar da yake wa al’ummar kasar nan.

Sai dai Jam’iyyar adawa ta PDP ta ce, borin kunya ce gwamnatin APC ke yi, saboda manuniya ta nuna cewar al’ummar kasar nan sun gaji da mulkinta.

Malam Abdul’aziz Abdul’aziz na ɗaya daga cikin masu magana da yawun Shugaban kasar ya bayyana cewa, ganin irin rawar da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ke takawa wajen gyara kurakuran da Jam’iyyar PDP ta yi ne tsawon shekara 16 da suka ɗauka.

“Suna mulki ne ya sa suke kaɗa gangar siyasa tun kafin lokacin ya zo.

“Su wadanda suke irin wadannan zarge-zargen ai su ne mutanen da suke ɗauke hankalin gwamnati daga kan abin da ya kamata ta yi”, in ji Abdul’aziz.

Shi kuwa mataimakin mai magana da yawun Jam’iyyar PDP, Alhaji Ibrahim Abdullahi ya ce, martanin na fadar shugaban ba komai ba ne illa shure-shure da baya hana mutuwa, wanda duk ya iske shinkafa a Naira 6,000 da PDP ta faɗi zabe, yanzu kuma yake sayen shinkafar nan kan Naira 100,000, lallai akwai ayar tambaya da ake cewa wai ana gyara a cewar Ibrahim.

Fadar shugaban ta ce, taron da suka gudanar ba komai ba ne illa na wadanda ba sa fatan ci gaban kasar nan da kuma son tunzura al’umma da barazana da kuma bayyana ra’ayoyin da za su durƙusar da dimokuradiyya.

Jam’iyyun hamayya na fama da rikice-rikicen cikin gida, lamarin da masana kan harkokin siyasa ke bayyanawa da cewa zai iya kawo musu tarnaƙi wajen haɗewar da suke niyyar yi.

A shekarar 2023 ce dai Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu ya yi nasarar doke Alhaji Atiku Abubakar na Jam’iyyar PDP a Zaɓen Shugaban kasa, inda aka samu wasu gwamnonin PDP da ake zargin sun yi wa Jam’iyyar APC aiki.

Yanzu dai hankali ya karkata ne wajen ganin irin wainar da za a toya a babban taron Jam’iyyar PDP, wadda ke kan gaba a sahun jam’iyyun adawa.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jam iyyar PDP

এছাড়াও পড়ুন:

 Tsoffin Ma’aikatan Hukumar Leken Asiri HKI  Mosad Sun Shiga Cikin Masu Kiran A Kawo Karshen Yaki Da Gaza

A daidai lokacin da ake ci gaba da takaddama a HKI dangane da wasikar da wasu sojojin sama su ka rubuta na sukar yakin Gaza, wasu tsoffin ma’aikatar hukumar leken asiri ta “Mosad” sun bi sawunhu.

Kafafen watsa labarum HKI sun ambaci cewa, fiye da tsoffin jami’an leken asirin kungiyar MOSAD 200 ne su ka rattaba hannu akan wata takarda suna nuna goyon bayansu da sojan sama da su ka yi kira a kawo karshen yakin Gaza.

Kwanaki kadan da su ka gabata, tashar talabijin din Channel 13; ta watsa labarin da yake cewa; Wasu ma’aikatar rundunar leken asiri ta soja sun shiga cikin masu kira da a kawo karshen yakin na Gaza da kuma dawo da fursunoni daga can.

An kuma samu irin wannan halayyar ta yin kira a kawo karshen yakin a tsakanin likitocin soja su 100 sai kuma malaman jami’a su ma daruruwa.

Kiraye-kirayen da sojojii suke yi a HKI da na kwo karshen yakin Gaza da mayar da fursunonin yaki, ya bude wata sabuwar takaddama a tsakanin ‘yan  siyasa.

Wasikar ta bude jayayya a tsakanin ‘yan sahayoniya akan cewa, Netanyahu yana ci gaba da yin yaki ne saboda maslahar kashin kansa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Aljeriya ta yi barazanar korar jami’an diflomasiyyar Faransa 12
  •  Tsoffin Ma’aikatan Hukumar Leken Asiri HKI  Mosad Sun Shiga Cikin Masu Kiran A Kawo Karshen Yaki Da Gaza
  • Xi Da Prabowo Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Sin Da Indonesiya
  • Al’ummar Mauritaniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Nuna Adawa Da Yakin Gaza
  • ’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa
  • Dagewa Iran Takunkuman Zalunci Na Daga Cikin Manufofin Tattaunawa Da Amurka: Aref
  • Jiragen Yakin Kasar Amurka Suna Rusa Cibiyoyin Ilmi A Hare-Haren Da Suke Kaiwa Kasar Yemen
  • Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba —Ganduje