Leadership News Hausa:
2025-03-25@20:13:46 GMT

‘Yan Asalin Nijeriya Da Ke Buga Wa Kasashen Turai Wasa

Published: 9th, February 2025 GMT

‘Yan Asalin Nijeriya Da Ke Buga Wa Kasashen Turai Wasa

Ga wasu manyan ‘yan kwallo da tauraronsu ke haskawa a duniya, wadanda asalin ‘yan Nijeriya ne, wato ko dai iyayensu baki daya ko wani daga cikin iyayen ‘yan Nijeriya ne.

 

Jamal Musiala (Jamus)

Matashin dan wasa Jamal Musiala, wanda aka haifa a ranar 26 ga Fabrairun shekarar 2003, fitaccen dan kwallon kasar Jamus ne da kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munich ta Jamus din kuma yana cikin matasan ‘yan kwallon da suke tashe a duniya a yanzu saboda ba za ka lissafa matasan ‘yan wasa guda biyar ba a duniya ba tare da ka saka sunansa ba.

An haife shi ne a garin Stuttgart da ke Jamus, amma mahaifinsa mai suna Daniel Richard asalin can Nijeriya ne, wanda ya yake da shaidar zama dan Ingila, mahaifiyarsa mai suna Carolina kuma ‘yar Jamus ce.

Matashi Musiala ya wakilci kasar Ingila a kwallon matakin yara, kafin ya koma Jamus da buga wasa sannan kuma ya lashe kofuna da dama irin su gasar Bundesliga guda hudu da sauran kofuna, sannan ya samu kyaututtuka da dama tun daga lokacin da kungiyar Bayer Munchen ta fara saka shi a wasa tun yana dan shekara 17 a duniya.

 

Karim Adeyemi

Karim-Dabid Adeyemi wanda aka haifa a ranar 18 ga watan Janairun shekarar 2002, dan wasan Jamus ne da kungiyar kwallon kafa ta Borussia Dortmund. An haifi dan wasan a birnin Munich, wanda mahaifinsa asalin dan Nijeriya ne, amma mahaifiyarsa ‘yar Romaniya ne kuma a kwanakin baya danwasan da ke buga wasa a Dortmund da ke Jamus ya kusa komawa kungiyar kwallon kafa ta Napoli ta kasar Italiya kafin daga baya cinikin ya rushe bayan yaki amincewa da tafiya.

A baya-bayan nan Karim Adeyemi ya bude wata gidauniya a Nijeriya kuma ya bude gidauniyar ne a birnin Ibadan da ke Jiyar Oyo a kudu maso yammacin kasar nan, inda ya ce gidauniyar za ta mayar da hankali kan koyar da wasanni da ilimi, sannan a lokacin da ya ziyarci Nijeriya, Adeyemi ya shaida wa manema labarai cewa nan gaba yana tunanin komawa buga wasa a gasar Premier ta Ingila.

 

Michael Olise

Shima matashin dan wasan an haife shi ne a ranar 12 ga Disamban 2001, dan kwallo da a yanzu yake wakiltar Faransa kuma yake buga wasa a kungiyar Bayern Munich ta kasar Jamus. Olise wanda ya koma Jamus da buga wasa daga kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace asalin mahaifinsa dan Nijeriya ne, amma mahaifiyarsa ‘yar Aljeriya ce mazauniyar Faransa. Kuma yanzu haka yana daya daga cikin matasan ‘yan wasan da tauraruwarsu take haskawa a nahiyar Turai.

 

Noni Madueke

Shi dai asalin sunansa shi ne Chukwunonso Tristan “Noni” Madueke, kuma an haife shi ne a ranar 10 ga Maris a shekarar 2002 kuma yanzu yana wakiltar kasar Ingila ne, sannan yana buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Chelsea ta Ingila kuma shima asalin mahaifinsa dan Nijeriya, amma shi a Ingila aka haife shi, sannan itama mahaifiyarsa ‘yar asalin kasar Ingila ce.

 

Bukayo Saka

Bukayo Saka fitaccen dan kwallo ne da a yanzu yake jan zarensa a kungiyar kwallon kafa ta Arsenal da ke Ingila kuma danwasan wanda asalin sunansa Bukayo Ayoyinka Temidayo Saka, iyayensa Adenike da Yomi Saka duka ‘yan Nijeriya ne kuma a baya ya sha bayyana cewa yana alfahari da kasancewarsa dan Nijeriya, kuma ya kan ziyarci kasar nan a wasu lokutan.

 

Ethan Chidiebere Nwaneri

Ethan Chidiebere Nwaneri wanda aka haifa a ranar 21 ga watan Maris na 2007, matashin danwasa ne da a yanzu yake tashe a kungiyar kwallon kafa ta Arsenal, kuma an haife shi ne a arewacin Landan, amma iyayensa ‘yan Nijeriya ne, sannan ya wakilci tawagar ‘yanwasan kasa da shekara 16 da 17 da 19 sai dai har yanzu ba wakilci babbar tawagar Ingila ba, wanda hakan ya sa za a iya gayyatarsa Nijeriya.

 

Joshua Orobosa Zirkzee

Tsohon dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Bologna dake kasar Italiya, Joshua Orobosa Zirkzee wanda aka haifa a ranar 22 ga Mayun 2001, dan kwallo ne da yake wakiltar kasar Netherlands, kuma yake buga wasa a yanzu a kungiyar kwallon kafa ta Manchester United ta Ingila sanann an haife shi ne a birnin Schiedam, sai dai shi mahaifiyarsa ce ‘yar Nijeriya, amma mahaifinsa dan Netherland ne.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a kungiyar kwallon kafa ta wanda aka haifa a ranar yan Nijeriya ne dan Nijeriya buga wasa a

এছাড়াও পড়ুন:

Wang Yi: Kasar Sin Na Da Kwarin Gwiwa Kan Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Japan Da Koriya Ta Kudu  

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya bayyana a jiya cewa, kasar Sin na dora muhimmanci sosai kan hadin gwiwar dake tsakanin kasarsa da kasashen Japan da Koriya ta Kudu, kuma tana da kwarin gwiwa kan hakan.

Wang ya bayyana hakan ne a lokacin da yake halartar taron firaministan kasar Japan Shigeru Ishiba a birnin Tokyo tare da ministocin harkokin wajen kasashen Japan da Koriya ta Kudu. Yana mai cewa, an fara hadin gwiwa tsakanin Sin da Japan da Koriya ta Kudu da wuri, inda aka samu sakamako da dama, kuma tana da babban tasiri, wadda ta taka muhimmiyar rawa wajen inganta fahimtar juna da hadin gwiwar moriyar juna a tsakaninsu.

Wakilin Musamman Na Xi Ya Halarci Bikin Rantsar Da Shugabar Namibiya Fadin Yankin Da Ke Fama Da Zaizayar Kasa Na Kasar Sin Ya Ragu A 2024 

Kazalika, dangantakar Sin da Japan da Koriya ta Kudu tana kara bunkasa, za a kara tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin. Bugu da kari, hadin gwiwarsu na kara zurfafa, kasashen yankin za su kara kaimi wajen tunkarar kalubale daban daban daga waje.

Wang ya kara da cewa, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da kasar Japan da Koriya ta Kudu, wajen kafa sahihiyar ra’ayi game da tarihin yakin duniya na biyu, da kiyaye tsarin bangarori daban daban, da kiyaye muhimmiyar rawar da MDD ke takawa a tsarin kasa da kasa, da ci gaba da inganta hadin gwiwa, da ba da gudummawa ga samun zaman lafiya da wadata a shiyyar da duniya baki daya. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Turkiyya Sun Bukaci kasashen Musulmi Su Magance matsalar Jinkai A Kasar Palasdinu Da Aka Mamaye
  • An Ceto ‘Yan Nijeriya Sama Da 950 Daga Gidajen Yari A Libya – Gwamnati
  • Lauyoyi 77 a Jamus sun yi kira ga gwamnati da ta mutunta sammacin ICC na cafke Netanyahu
  • Sin Ta Sanar Da Dokar Dakile Takunkuman Kasashen Waje
  • Yaushe Ronaldo Zai Daina Jefa Kwallo A Raga?
  • Iran ta yi gargadin cewa keta hurumin Lebanon da Isra’ila ke yi barazana ne ga zaman lafiyar duniya
  • Iran Ce Kasar Wacce Ta Fi Shigar Da Kayakin Kasuwanci Zuwa Kasar Afganistan A Shekarar Da Ta Gabata
  • Ko Raunin ‘Yan Wasa Zai Rage Wa Barcelona Karsashi A Kakar Bana?
  • Isra’ila : ‘Yan adawa sun kira zanga-zangar gama-gari bayan korar shugaban Shin Bet
  • Wang Yi: Kasar Sin Na Da Kwarin Gwiwa Kan Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Japan Da Koriya Ta Kudu