Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Fara Janyewa Daga Yankin Netzarim Da Ke Zirin Gaza
Published: 9th, February 2025 GMT
Sojojin mamayar Isra’ila sun fara janyewa daga yankin Netzarim da ke tsakiyar Zirin Gaza
Kafofin yada labaran haramtacciyar kasar Isra’ila sun tabbatar da cewa: Sojojin mamayar Isra’ila za su fara ficewa daga yankin Netzarim da ke tsakiyar Zirin Gaza a daren jiya.
Jaridar Yedioth Ahronoth ta haramtacciyar kasar Isra’ila ta watsa rahoton cewa: Rundunar sojin mamayar Isra’ila ta ba da umarnin ficewa daga yankin Netzarim da ke tsakiyar Gaza a wani bangare na aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin kungiyar Hamas da gwamnatin mamayar Isra’ila a yankin.
Jaridar ta bayyana cewa: Runduna ta 162 ta sojojin mamayar ta sake matsawa zuwa kusa da kan iyaka da kuma janyewa daga yankin Netzarim na nufin cewa, babu sojojin mamayar Isra’ila a arewacin Zirin Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: daga yankin Netzarim da mamayar Isra ila
এছাড়াও পড়ুন:
Matasa 4 Sun Yi Garkuwa Da Yaro, Sun Kashe Shi A Bauchi
Likitoci sun tabbatar da mutuwarsa, daga nan aka bai wa iyalansa gawarsa domin yin jana’iza.
Kakakin ‘yansandan Bauchi, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce suna samun labarin lamarin, jami’ansu suka fara bincike, musamman a wajen POS da ke kusa da inda aka nemi a biya kuɗin fansar.
A yayin binciken, sun kama wani matashi mai shekara 23, Rabi’u Muhammadu daga ƙauyen Leka, wanda lambar wayarsa aka yi amfani da ita wajen kira mahaifin yaron.
Sun kuma gano asusun bankin da aka bayar don a biya kuɗin fansar.
Da aka tambayi Rabi’u, ya bayyana cewa Samson Ozoichikel, mai shekara 35 daga ƙauyen Sade, shi ne ya shirya yin garkuwa da yaron.
Sannan ya ambaci wasu matasa biyu, Muhammad Sani (Jingi) mai shekara 25 da Musa Usman (Kala) mai shekara 30, dukkaninsu daga ƙauyen Leka.
A halin yanzu, ‘yansanda sun tsare waɗanda ake zargi, kuma ana zurfafa bincike a sashen manyan laifuka (SCID).
Kwamishinan ‘yansandan Bauchi ya tabbatar da cewa za su yi duk mai yiwuwa domin ganin an yi adalci.
Ya kuma roƙi jama’a da su ci gaba da bai wa rundunar haɗin kai da kuma sanar da ‘yansanda duk wani abu da suke zargi a layin gaggawa na 112 ko Police Control Room a lamba 08156814656.
Rundunar ‘yansandan Bauchi ta jaddada cewa tana nan daram domin kare rayuka da dukiyar al’umma.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp