HausaTv:
2025-04-13@09:52:24 GMT

Hukumar Falasdinawa Ta Mayar Da Martani Kan Mafarkin Gwamnatin Mamayar Isra’ila

Published: 9th, February 2025 GMT

Falasdinawa sun fitar da martanin farko mai gauni kan kalaman fira ministan ‘yan mamayar Isra’ila dangane da furucinsa ga Saudiyya

Kungiyar ‘yantar da Falasdinu ta yi Allah wadai da kalaman da fira ministan mamayar Isra’ila Benjamin Netanyahu ya yi game da kafa kasar Falasdinu a cikin kasar Saudiyya.

Sakataren kwamitin zartarwa na kungiyar ‘yantar da Falasdinu Hussein Al-Sheikh ya bayyana cewa: Suna yin Allah wadai da matakin da mahukuntan yahudawan sahayoniyya suka dauka na kai cin mutunci da raina kimar masarautar Saudiyya da ‘yancinta, wanda suka yi kira da a kafa kasar Falasdinu a kasar Saudiyya, kuma wannan furuci na Rashin tunani ya yi cin karo da dokokin kasa da kasa da yarjejeniyar kasa da kasa.

Ya kara da cewa: Suna tabbatar da cewa: Kasar Falasdinu za ta kasance ce a kasar Falasdinu kawai, kuma suna jinjinawa matsayin masarautar Saudiyya da jagorancinta da al’ummarta, wadanda a kullum suke kira jaddada kare jaddada dokokin kasa da kasa da kuma kudurin samar da kasashe biyu na Falasdinawa da na yahudawan sahayoniyya a matsayin tushen samar da tsaro, kwanciyar hankali da zaman lafiya a yankin.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Falasdinu

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu

Shugaban hukumar makamashin nukliya na kasar Iran ya ce kasashen wamma suna son kebe kansu da fasahar nukliya a tsakaninsu.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Muhammad Eslamu shugaban hukumar AEOI yana fadar haka a jiya Jumma’a ya kuma kara da cewa kamfanin makamashin nukliya na kasar Iran ya kafa a kasar Iran kuma ba wanda ya isa ya kauda shi. Sabanin abinda kasashen yamma suke so na hana sauran kasashen duniya mallaka fasahar nukliya, da kuma dogara da su kadai, su bada abinda suka ga dama ko  su hana gaba daya.

Ya ce JMI ta wuce wasu kasashen yamma a ayyuka da kuma sani da sarrafa makamashin Uranium, wanda ya tada hankalin wadannan kasashe, kuma suke sun han awasu kasashen duniya bin sawun kasar Iran na zama yentattu a wannan fage.

Islami ya kara da cewa kamfanin makamashin nukliya na kasar Iran ya kai wani matsayinda yana taiamakawa sauran kamfanoni na cikin gida ba tare da bukatar dogaro da kwararru ko kuma taimakon kasashen waje ba. Ya ce a halin yanzu iran na samar da wutan lantarki mai karfin magewats 20,000 tare da Makamashin Nukliya.

     

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Burkina Faso Ya Yi Fatali Da Tayin Saudiyya Na Gina Masallatai 200 A Kasarsa
  • Sama da mutane 1,560 ne sukayi shahada tun bayan da Isra’ila ta koma kai farmaki Gaza
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • Sin Ta Yi Allah-wadai Da Karin Harajin Amurka Ta Kuma Jaddada Goyon Bayanta Ga Ka’idojin WTO 
  • Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu
  • Hizbullah ta kirayi gwamnatin Lebanon da ta dauki mataki kan hare-haren Isra’ila
  •  Sojojin HKI Sun Yi Kisan Kiyashi A Yankin Shuja’iyya
  • Za a mayar da tubabbun ’Yan Boko Haram cikin al’umma – Gwamna Buni
  • Jami’an Amurka da na Saudiyya sun tattauna batutuwan da suka shafi Gaza da yankin
  • Macron :  Faransa na shirin amincewa da yankin Falasdinawa a matsayin kasa