Wakilin Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci A Iraki Ya Ya Jaddada Rawar Juyin Juya Halin Musulunci
Published: 9th, February 2025 GMT
Wakilin Jagoran juyin juya halin Musulunci a kasar Iraki ya ce: Juyin juya halin Musulunci ya gabatar da wani sabon samfuri na hadin kan al’umma
Ayatullah Mojtaba Hosseini, wakilin Jagoran juyin juya halin Musulunci a kasar Iraki ya bayyana muhimmancin hadin kan al’ummar musulmi da kuma nauyin da ya rataya a wuyan musulmi na daidaiku da na al’umma dangane da manufofin juyin juya halin Musulunci, yana mai cewa: juyin juya halin Musulunci ya gabatar da wani sabon salo na hadin kan al’ummar musulmi.
A jawabin da ya gabatar na zagayowar samun nasarar juyin juya halin Musulunci a Iran da aka gudanar a tsohon gidan da Imam Khumaini (r.a) da ya zaune a birnin Najaf, Ayatullah Husaini ya jaddada muhimmancin hadin kan al’ummar musulmi da kuma irin nauyin da ke wuyan musulmi na daidaiku da na zamantakewa da suka dace da manufofin juyin juya halin Musulunci.
Har ila yau Ayatullah Mojtaba Hosseini ya tabo batun juyin juya halin Musulunci a Iran yana mai bayyana hakan a matsayin wata mu’ujiza ta Ubangiji, sannan ya kara da cewa: Batun juyin juya halin Musulunci yana nan a kan tafarkinsa kuma Allah ya nufa ya zama wani gagarumin yunkuri na jama’a wanda ya iya haifar da gagarumin sauyi a Iran da kuma duniyar musulmi.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: juyin juya halin Musulunci a
এছাড়াও পড়ুন:
Jihar Kano Ta Samar Da Wani Salo Na Bunkasa Ilmin Addinin Musulunci A Jihar
Gwamnatin jihar Kano ta dauki wani gagarumin mataki na bunkasa ilimin addinin musulunci a jihar ta hanyar hada hannu da kungiyar Agaji ta Musulunci da ke Birtaniya, wato Muslim Charity For United Kingdom a turance.
Wannan haɗin gwiwar na nufin tallafa wa makarantun Islamiyya da kayayyakin koyon ilimi na zamani, da sauransu.
A cewar daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar ilimi ta jihar Kano, Balarabe Abdullahi Kiru, wannan shiri ya yi daidai da kokarin da gwamnati ke yi na karfafa fannin ilimi.
Haɗin gwiwar zai magance matsalolin da ke addabar ilimin addinin Islama, da tabbatar da cewa makarantun Islamiyya sun sami tallafin da ya dace don samu ingantaccen yanayin karatu da koyarwa.
Ya yi nuni da cewa, Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dakta Ali Haruna Makoda, ya bayyana fatan cewa, wannan hadin gwiwa zai inganta ilimin addinin Musulunci, musamman a tsarin makarantun Islamiyya.
Ya ce, shirin zai mayar da hankali ne wajen samar da kayayyakin koyo na zamani domin inganta kwazon dalibai.
Da take jawabi a madadin tawagar, shugabar kungiyar agaji ta addininMusuluncida ke Birtaniya, Dr. Samira Abubakar Abdullahi, ta bayyana cewa kungiyar na aiki tukuru a Najeriya domin tallafawa harkokin ilimi da kiwon lafiya.
Ta bayyana cewa gudummawar da suke bayarwa sun hada da shirye-shiryen gyara makarantu, ayyukan ci gaban ilimi, da ayyukan kiwon lafiya.
“Mun zo ma’aikatar don tattaunawa kan bangarorin haɗin gwiwa da kuma yi wa kwamishina bayani game da ayyukanmu,” inji ta.
Kungiyar agajin tana aiki tukuru a Najeriya don tallafawa ayyukan ilimi da kiwon lafiya.
Daga Khadija Aliyu