Aminiya:
2025-04-18@23:16:42 GMT

Gwamnatin Kano ta dakatar wani fim mai suna Zarmalulu

Published: 9th, February 2025 GMT

Gwamnatin Kano ta dakatar da wani fim da take zargin ya saɓa ka’ida tare da gayyatar dukkannin wanda suka fito a cikinsa domin sauraron ba’asi.

Hukumar tace fina-finai da dab’i ta Kano ce ta dakatar da fim ɗin mai suna Zarmalulu bayan ƙorafin da aka miƙa mata.

Taron Qur’ani: Tsakanin magoya baya da masu kushe Me ya sa ake musayar yawu tsakanin APC da PDP?

Wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar a ranar Asabar, ta ce ana zargin waɗanda suka shirya fim ɗin sun sanya masa suna na baɗala.

“Biyo bayan ƙorafin da Hukumar ta karɓa daga wasu masu kishin Jihar Kano akan wannan fim ɗin, Shugaban Hukumar, Abba El-Mustapha ya bayyana damuwarsa kan lamarin tare da dakatar da fim ɗin.

“Haka kuma, Abba El-Mustapha ya gayyaci dukkannin wanda suka fito a shirin domin jin ba’asi na yin amfani da ita wannan kalma.”

Bayanai sun ce fim ɗin mai suna “Zarmalulu” ana zarginsa da rashin ma’ana sannan an yi masa laƙabi da wani suna mai kama da na baɗala.

Hukumar ta buƙaci duk waɗanda suka yi ruwa da tsaki a fim ɗin da su bayyana a gaban kwamatin bincike da ta kafa.

Hukumar tace fina-finan na da hurumin dakatar da dukkannin wani fim da bata gamsu da yadda aka shirya shi ba tare da ladaftar da duk wani da ta samu da yin abinda bai kamata a cikin kowane fim ba ko kuma a wajen fim ɗin matsawar ɗan Masana’antar Kannywood ne.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hukumar Tace Fina Finai Jihar Kano kannywood Zarmalulu

এছাড়াও পড়ুন:

 Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Hare-hare A Kudancin Lebanon

Sojojin HKI suna cigaba da kai hare-hare a yankunan kudancin Lebanon da ya zama ruwan dare a cikin kwanakin bayan nan.

A jiya Laraba jiragen yakin HKI sun kai hare-hare a gari “Aytas-sha’ab. Haka nan kuma tankokin yakin ‘yan mamayar sun kai wasu hari a kan wasu gidaje a garin na Aytas-sha’ab.

Haka nan kuma sojojin mamayar sun gina wata Katanga da ta raba tsakanin Ayta da Khillatul-wardi.

Har yanzu sojojin na HKI suna ci gaba da zama a cikin wasu wurare biyar da ta ki ficewa daga cikinsu bayan zuwa karshen wa’adin kwanaki 60 daga tsagaita wutar yaki.

Kamfanin dillancin labarun Lebanon ya bayyana cewa; Jirgin yakin HKI maras matuki ya kai hari akan gidajen tafi da gidanka da wadanda aka rushewa gidaje suke ciki a kusa da garin Shaihin. Sai dai babu wani rahoto akan rashin rai,ko jikkatar mutane, sai dai gidaje da dama sun rushe.

Wadannan hare-haren suna a matsayin sabon bude wuce gona da iri na HKI a kudancin Lebanon.

Kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon din ta sha yin kira ga gwamnati da ta yi aiki da nauyin da ya rataya a wuyanta na tilasata wa ‘yan mamaya janyewa daga wuraren da suke ciki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kashe Mutane Fiye Da 300 A Wani Kazamin Fada A Yankin Darfur Da Ke Yammacin Kasar Sudan
  • Yara Kimani 3,500 Ne Suka Rasa Rayukansu A Taken Medeteranin A Shekaru 10 Da Suka Gabata
  • Majalisar Dokokin Zamfara Ta Dawo da Dan Majalisa Basko da Aka Dakatar
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Taron Ƙarawa Ma’aikatan Jinƙai Sani A Jihar Kano
  •  Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Hare-hare A Kudancin Lebanon
  • Hisbah ta kama matashi yana ‘baɗala’ da Akuya a Kano
  • An Kashe Mutane 7 A Yayin Da ‘Yan Ta’adda Suka Ƙaddamar Da Wani Sabon Hari A Adamawa
  • KADGIS Za Ta Yi Amfani Da Sabuwar Manhajar Biyan Diyyar Filaye A Kaduna
  • KADGIS Ta Samar Da Sabuwar Manhajar Biyan Diyyar Filaye A Kaduna
  • Matashi ya kai kansa ofishin ’yan sanda