Gwamnatin Kano ta dakatar da wani fim mai suna Zarmalulu
Published: 9th, February 2025 GMT
Gwamnatin Kano ta dakatar da wani fim da take zargin ya saɓa ka’ida tare da gayyatar dukkannin wanda suka fito a cikinsa domin sauraron ba’asi.
Hukumar tace fina-finai da dab’i ta Kano ce ta dakatar da fim ɗin mai suna Zarmalulu bayan ƙorafin da aka miƙa mata.
Taron Qur’ani: Tsakanin magoya baya da masu kushe Me ya sa ake musayar yawu tsakanin APC da PDP?Wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar a ranar Asabar, ta ce ana zargin waɗanda suka shirya fim ɗin sun sanya masa suna na baɗala.
“Biyo bayan ƙorafin da Hukumar ta karɓa daga wasu masu kishin Jihar Kano akan wannan fim ɗin, Shugaban Hukumar, Abba El-Mustapha ya bayyana damuwarsa kan lamarin tare da dakatar da fim ɗin.
“Haka kuma, Abba El-Mustapha ya gayyaci dukkannin wanda suka fito a shirin domin jin ba’asi na yin amfani da ita wannan kalma.”
Bayanai sun ce fim ɗin mai suna “Zarmalulu” ana zarginsa da rashin ma’ana sannan an yi masa laƙabi da wani suna mai kama da na baɗala.
Hukumar ta buƙaci duk waɗanda suka yi ruwa da tsaki a fim ɗin da su bayyana a gaban kwamatin bincike da ta kafa.
Hukumar tace fina-finan na da hurumin dakatar da dukkannin wani fim da bata gamsu da yadda aka shirya shi ba tare da ladaftar da duk wani da ta samu da yin abinda bai kamata a cikin kowane fim ba ko kuma a wajen fim ɗin matsawar ɗan Masana’antar Kannywood ne.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hukumar Tace Fina Finai Jihar Kano kannywood Zarmalulu
এছাড়াও পড়ুন:
Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Bauchi, ta kama wasu matasa huɗu da ake zargi da yin garkuwa da kuma kashe wani yaro ɗan shekara shida, Shuaibu Safiyanu, a ƙauyen Sade da ke Ƙaramar Hukumar Darazo.
Aminiya ta ruwaito cewar mahaifin yaron, Safiyanu Abdullahi ne, ya sanar da Sarkin garinsu, Musa Isah, cewa a ranar 20 ga watan Maris, 2025, ɗansa ya ɓace.
Ɗan sa-kai ya kashe matasa biyu a Borno Gwamnatin Jigawa ta ƙaddamar da shirin noman rani na LallashiWashegari, wani ya kira shi a waya yana neman kuɗin fansa.
Da farko, ya nemi miliyan uku (₦3,000,000), amma daga baya suka rage zuwa Naira dubu ɗari biyu (₦200,000).
A ranar 21 ga watan Maris, aka gano gawar yaron a cikin daji, an ɗaure masa wuya da igiya.
Nan take aka kai shi asibiti, inda likitoci suka tabbatar da mutuwarsa.
Daga nan aka bai wa iyalansa gawarsa domin yi masa jana’iza.
Kakakin ’yan sandan Jihar, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce bayan samun rahoton lamarin, jami’an su suka fara bincike.
Sun fara binciken ne daga wajen POS da ke kusa da inda aka buƙaci a biya kuɗin fansar.
A yayin binciken, sun kama wani matashi mai shekara 23, Rabi’u Muhammadu daga ƙauyen Leka.
An gano cewa lambar wayarsa ce aka yi amfani da ita wajen kiran mahaifin yaron.
Sannan ’yan sanda sun gano asusun bankin da aka bayar don biyan kuɗin fansar: Lambar asusu: 0145285130 Sunan mai asusu: Ozochikelu Samson Banki: Union Bank PLC
Bayan kama Rabi’u, ya bayyana cewa Samson Ozochikel, mai shekara 35 daga ƙauyen Sade, shi ne ya shirya yadda za a sace yaron.
Ya kuma ambaci wasu matasa biyu, Muhammad Sani (Jingi), mai shekara 25, da Musa Usman (Kala), mai shekara 30, dukkaninsu daga ƙauyen Leka.
A halin yanzu, ’yan sanda suna tsare da su, kuma ana ci gaba da bincike a sashen binciken manyan laifuka (SCID).
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, ya tabbatar da cewa za su tabbatar da an yi adalci.
Ya kuma roƙi jama’a da su ci gaba da bai wa ’yan sanda haɗin kai, tare da sanar da su duk wani abun zargi ta layin kiran wayar gaggawa 112 ko Police Control Room a lamba 08156814656.
Rundunar ta jaddada ƙudirinta na kare rayuka da dukiyar al’ummar jihar.