Leadership News Hausa:
2025-04-15@14:20:48 GMT

Me Dakatarwar Da Pillars Ta Yi Wa Usman Abdalla Ke Nufi?

Published: 9th, February 2025 GMT

Me Dakatarwar Da Pillars Ta Yi Wa Usman Abdalla Ke Nufi?

A ranar Lahadi ne mahukuntan kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars suka bayar da sanarwar dakatar da mai koyarwa, Usman Abdallah mako uku, sakamakon rashin kokarin kungiyar a baya bayan nan a bana da kuma nuna halin rashin hakuri ga magoya bayan kungiyar a lokacin da aka tashi daga wasan da kungiyar ta tashi canjaras da kungiyar Bayelsa United a filin wasa na Sani Abacha dake kofar mata a Kano.

A wata sanarwa da aka fitar a shafin sada zumunta na facebook, kungiyar ta ce kociyan ya nuna halin rashin da’a, bayan tashi ba ci a wasa da Bayelsa ba kuma halayyar da ya nunawa magoya baya ba ta dace ba saboda a matsayinsa na mai koyarwa dole ne sai ya jure duk wani surutu da magoya baya za su yi masa. Pillars ta kasa hawa kan ganiya a ‘yan wasannin baya bayan nan, wadda ta yi nasara daya daga karawa uku a gasar ta Premier Nijeriya.

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (6) Saudiyya Ta Yi Watsi Da Shirin Fitar Da Falasdinawa Daga Gaza

Hakan ne ya sa shakku ga mahukuntan Pillars da magoya baya kan rashin kokarin kungiyar da abin da hakan zai haifar kuma bayan tashi daga wasan da Bayelsa a wasan mako na 24 ranar Lahadi, mahukuntan suka ce ba za su lamunci rashin da’a daga Usman Abdalla ba da ya yi wa magoya bayanta, hakan ya sa aka dauki mataki a kansa kuma ya fara aiki nan take.

Tuni aka bai wa Ahmed Yaro-Yaro aikin rikon kwarya, inda Abubakar Musa da Gambo Muhammad da Suleiman Shu’aibu da kuma Ayuba Musa za su taimaka masa. Kano Pillars za ta je Remo Stars a wasan gaba na mako na 24 a babbar gasar firimiya ta Nijeriya.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: magoya baya

এছাড়াও পড়ুন:

A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi

Sakamakon gazawar shugabanci, bayar da tallafi na neman zama wani bangare a tarihin dimokoradiyyar Nijeriya, inda gwamnatocin jihohi da ’yan majalisu da sauran ’yan siyasa suke amfani da shi wajen cusa wa ’yan kasa ra’ayinsu na siyasa.

A duk lokacin da al’umma suka koka a kan wani mummunann yanayi da ya hada da matsin tattalin arziki da gobarar tankar mota da ambaliyar ruwa da gobara, abin da yake biyo baya shi ne gwamnati ta raba tallafin shinkafa da sauaran kayan abinci, tamkar shinkafa ita ce maganin duk wata matsala. A wasu lokutan, a kan raba babura masu kafa uku da dabbobi a matsayin tallafi.

Makudan kudaden da gwamnatoci suke kashewa da sunan bayar da tallafi, inda ba a ganin tasirin hakan a rayuwar ’yan kasa, lamari ne da ke ci gaba da damun ’yan Nijeriya. Alal misali, makudan kudaden da gwamnatocin jihohi arewa suka ware da sunan ciyarwar watan Ramadana ya saha suka daga ’yan kasar da dama, cikinsu har da masu amfana da ciyarwar.

A yayin da Gwamnatin Jigawa ta sanar da kashe Naira biliyan 4.8, ita kuwa Gwamnatin Kano ta ware Naira biliyan 8 domin ciyarwar Ramadanan 2025. Gwamnatin Sakkwato ta ware Naira biliyan 6.7, yayin da Gwamnatin Kebbi ta ware Naira biliyan 1.5, inda Gwamnatin Neja ta ware Naira miliyan 976. A nata bangaren, Gwamnatin Yobe ta ware Naira miliyan 298. Uwa-uba, Gwamnatin Katsina ta ware Naira biliyan 10 duk don ciyarwar watan Ramadana.

Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu ’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa

Damuwar da masu ruwa da tsaki suka bayyana ita ce yadda gwamnatocin suka kashe wadannan makudan kudade da sunan shirin ciyarwar Ramadana. Misali, shirin ciyarwar Gwamnatin Jigawa an yi hadin gwiwa ne tsakanin gwamnatin jihar da kananan hukumomi bisa kaso 55 da 45. Rashin tabbacin da ke tattare da wannan shiri shi ne su wane ne ainihin wadanda suka amfana da wannan shiri na ciyarwa, sannan kuma wanne tsari aka bi wajen rabo?

A wata ziyar ba-zata da Gwaman Jihar Jigawa ya kai daya daga wuraren ciyarwar a karamar Hukumar Dutse a Ramadanan da ya gabata, ya nuna rashin gamsuwarsa dangane da tsarin da ya gani, wanda hakan ya tabbatar da sukar da al’umma suke yi a kan rashin tsarin shirin ciyarwar. Gwamna Namadi ya nuna rashin amincewarsa game da rashin tsari da karancin abincin a cibiyoyi 609 da aka tsara za su bayar da abinci kala uku ga masu rauni da talakawa 182,700 a kullum. Ya koka da cewa, ‘‘Ban gamsu ba, kodayake ban yi mamaki ba da rashin tsari da sakacin da na gani ba a yau. Ba zai yiwu ba wasu ’yan tsiraru su hana mutanenmu amfana da abin da suka cancanci su samu ba.’’

Duba da irin yadda aka tafiyar da shirin ciyarwar Ramadana, shirin cike yake da almubazaranci da kudin al’umma. Rashin tartibiyar hanyar tabbatar da wadanda suka amfana da shirin, ita ce ta ba wa cin-hancin kofar shigowa. Wannan wata sabuwar hanyar satar kudin al’umma ce cikin sauki da sunan bayar da tallafi, da ya kunshi ciyar da masu rauni a watan Ramadana.

A yayin da ba za a sa kafa a shure irin rawar da bayar da tallafin gwamnati yake takawa ba a yanayi na gaggawa, masu rauni da talakawa za su fi amfana, idan aka saka wadannan makudan kudade a harkar noma da samar da aikin yi ga matasa da mata da samar da kanan masana’antu, wadanda za su samar da mafita ta dindindin. Gwamnati ta yi wa bayar da tallafi mummunar fahimta, duba da yadda ta ba shi muhimmanci, wanda hakan ke nuna dalilin da ya sa aka kasa warware matsalolin kasa yadda ya kamata.

Ya kamata bayar da tallafi ya zamto saboda wasu dalilai na musamman, da nufin bayar da agaji na wucin-gadi, ba samar da mafita ta dindindin ba ga muhimman matsalolin kasa kamar talauci da rashin aikin yi ba. Ana bayar da tallafi ne ga mutanen da suke cikin yaki kamar a yankin Sudan da Gaza.

Shugabanni, musamman gwamnonin jihohi sun fi fifita raba tallafi a al’amuansu na gwamnati, ta yadda kusan ya zama wata hanya ta kimanta ayyukan zababbun masu rike da mukaman gwamnati, duk dai saboda sun gaza fahimtar yadda ake kimanta matsayin tattalin arzikin mutane, wanda ya hada da talauci da tallafi.

Ware makudan kudade domin ciyarwar watan Ramadana ba ita ce hanyar da ta dace ba wajen shawo kan matsalar tattalin arziki da ’yan kasa suke fuskanta. Samar da mafita ta wucin-gadi ko bayar da tallafi ta hanyar ciyarwa ko raba babura ba ita ce tartibiyar hanyar shawo kan matsalar ba. Ana yakar talauci da rashin aikin yi ne ta hanyar ba wa ’yan kasa horo, ba tallafin kaya ba.

Babu wata kasa da ta ci gaba ta hanyar raba kayan tallafi. Shugabanni suna cutar ’yan Nijeriya ne ta hanyar fifita bayar da kayan tallafi, da nufin yin awon gaba da kudin al’umma, wadanda sun isa su samar da mafita ta dindindin ga matsalolin zamantakewa da tattalin arzikin Nijeriya.

Bisa ga irin dimbin arzikin da kasar nan take da shi, da ya hada da yawan mutane, wadda wata dama ce ta rage talauci da rashin aikin yi, inda ’yan Nijeriya, musamman matasa suke bukatar horo fiye da raba kayan tallafi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan Najeriya sun koka kan rashin ingancin shinkafar Gwamantin Tarayya
  • Jama’a sun koka kan rashin inganci shinkafar Gwamanti a Kogi
  • Duk da samun koma baya: Najeriya ce kasa mafi arzikin danyen mai a Afirka —OPEC
  • Ministan Harkokin Noma Na Kasar Iran Ya Kama Hanya Zuwa Kasar Brazil
  • Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Sun Yi Fatan Al-Khairi Ga Iran Da Amurka A Tattaunawar Shirin Nukliyar Kasar
  • A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi
  •  Nigeria: Wani Bom Da Ya Tashi A Maiduguri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 7
  • Sin Da Sifaniya Sun Daga Matsayin Hadin Gwiwa A Fannin Shirya Fina-finai
  • Newcastle Na Gab Da Samun Gurbi A Gasar Zakarun Turai
  • Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo