Leadership News Hausa:
2025-03-25@20:20:37 GMT

Me Dakatarwar Da Pillars Ta Yi Wa Usman Abdalla Ke Nufi?

Published: 9th, February 2025 GMT

Me Dakatarwar Da Pillars Ta Yi Wa Usman Abdalla Ke Nufi?

A ranar Lahadi ne mahukuntan kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars suka bayar da sanarwar dakatar da mai koyarwa, Usman Abdallah mako uku, sakamakon rashin kokarin kungiyar a baya bayan nan a bana da kuma nuna halin rashin hakuri ga magoya bayan kungiyar a lokacin da aka tashi daga wasan da kungiyar ta tashi canjaras da kungiyar Bayelsa United a filin wasa na Sani Abacha dake kofar mata a Kano.

A wata sanarwa da aka fitar a shafin sada zumunta na facebook, kungiyar ta ce kociyan ya nuna halin rashin da’a, bayan tashi ba ci a wasa da Bayelsa ba kuma halayyar da ya nunawa magoya baya ba ta dace ba saboda a matsayinsa na mai koyarwa dole ne sai ya jure duk wani surutu da magoya baya za su yi masa. Pillars ta kasa hawa kan ganiya a ‘yan wasannin baya bayan nan, wadda ta yi nasara daya daga karawa uku a gasar ta Premier Nijeriya.

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (6) Saudiyya Ta Yi Watsi Da Shirin Fitar Da Falasdinawa Daga Gaza

Hakan ne ya sa shakku ga mahukuntan Pillars da magoya baya kan rashin kokarin kungiyar da abin da hakan zai haifar kuma bayan tashi daga wasan da Bayelsa a wasan mako na 24 ranar Lahadi, mahukuntan suka ce ba za su lamunci rashin da’a daga Usman Abdalla ba da ya yi wa magoya bayanta, hakan ya sa aka dauki mataki a kansa kuma ya fara aiki nan take.

Tuni aka bai wa Ahmed Yaro-Yaro aikin rikon kwarya, inda Abubakar Musa da Gambo Muhammad da Suleiman Shu’aibu da kuma Ayuba Musa za su taimaka masa. Kano Pillars za ta je Remo Stars a wasan gaba na mako na 24 a babbar gasar firimiya ta Nijeriya.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: magoya baya

এছাড়াও পড়ুন:

Ana ci gaba da gudanar da zanga-zangar goyon bayan Falastinu a kasashen duniya

Dubban mutane ne a birnin Amman babban birnin kasar Jordan suka gudanar da zanga-zanga bayan sallar Juma’a domin yin Allah wadai da sake dawo da laifukan da Isra’ila ke aikatawa a Gaza.

A rahoton factjo, dubban mutane sun bayyana goyon bayansu ga al’ummar Gaza a wani gagarumin maci na wannan Juma’a.

Mahalarta tattakin sun yi Allah wadai da hare-haren da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai kan masallacin Al-Aqsa a cikin watan Ramadan.

 A cikin wannan maci da aka gudanar bisa gayyatar Harkar Musulunci da kwamitin Tallafawa Falastinawa suka kira, dubban mutane sun halarta da suka hada da wakilai na siyasa, jam’iyyu, da kungiyoyin kwadago, da sauran jama’ar kasa, inda suka yi ta rera taken la’antar ayyukan zalunci na gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila, da kuma kin amincewa da duk wata makarkashiyar da aka kulla domin korar Falastinawa daga yankunansu.

Haka nan Wadanda suka halarci tattakin sun yi Allah wadai da kisan kiyashin da ake ci gaba da yi a zirin Gaza, tare da yin kira ga gwamnatocin kasashen Larabawa da na Musulunci da su dauki matakin gaggawa na dakatar da wannan aika-aikar da Isra’ila ke yi.

Mahalarta tattakin na nuna alhinin shahadar Abu Hamza, kakakin rundunonin Quds Brigade, sun yaba da karfin azamarsa da jajircewarsa, da sadaukar da ransa da jininsa saboda ‘yancin al’ummarsa.

Masu zanga-zangar sun kuma yi Allah wadai da cin amanar Amurkawa, wadanda suka bai wa makiya yahudawan damar soke yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kuma ci gaba da kashe al’ummar Gaza, tare da bayyana  gwamnatin Amurka a matsayin wadda take daukar nauyin wannan laifi ta hanyar aika bama-bamai da makamai masu linzami ga Isra’ila domin  kisan Falastinawa a zirin Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas : Isra’ila ta yi amfani da sulhu wajen tattara bayanai kan shugabannin Hamas domin kashe su
  • Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi
  • Juventus ta sallami kocinta Thiago Motta
  • Juventus za ta sallami kocinta Thiago Motta
  • Yaushe Ronaldo Zai Daina Jefa Kwallo A Raga?
  • An yi wa Jakadan Afirka ta Kudu da Amurka ta kora tarbar Jamurumai bayan komawarsa gida
  • Ana ci gaba da gudanar da zanga-zangar goyon bayan Falastinu a kasashen duniya
  • Babban Kusa A Kungiyar Hamas Salah Al-Bardawil Ya Yi Shahada
  • Gobara ta tashi a gidan mai sakamakon fashewar tanka a Neja
  • Ko Raunin ‘Yan Wasa Zai Rage Wa Barcelona Karsashi A Kakar Bana?