Aminiya:
2025-03-23@22:32:20 GMT

Gobara ta ƙone motoci da shaguna a wajen sayar da gas a Neja

Published: 9th, February 2025 GMT

Wata gobara da ta tashi a wajen sayar da gas a Sabon Wuse da ke Ƙaramar Hukumar Tafa a Jihar Neja, ta yi sanadin ƙonewar motoci da shaguna da kuma kayan abinci.

Lamarin ya faru ne a daren ranar Asabar lokacin da wata tanka ke sauke gas a wajen sayar da gas.

Gwamnatin Kano ta dakatar da wani fim mai suna Zarmalulu Me ya sa ake musayar yawu tsakanin APC da PDP?

Wutar ta ɗauki sa’o’i tana ci kafin isowar jami’an kashe gobara.

Wani mazaunin garin, Abdul Sabon-Wusa, ya ce bindigar ta girgiza yankin, inda mutane suka firgita suka fito daga gidajensu domin neman mafaka.

Wutar ta kuma bazu zuwa wani gidan mai, inda ta ƙone shaguna da motoci da aka ajiye.

“Muna godiya ga Allah ba a rasa rai ba, kuma ba a samu wanda ya jikkata ba.

“Idan hakan ta faru da rana lokacin da mutane ke kasuwancinsu, da wani babban iftila’in ne zai faru,” in ji shi.

Ya ce hayaƙin gobarar ya tashi sama sosai har ana iya ganinsa daga sassa daban-daban na garin, wanda ke nuna yadda wutar ta yi ƙamari.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara Wajen Sayar Gas

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan daba sun hallaka matashi ana sallar Tahajjud a Kaduna

Wasu da ake kyautata zaton ’yan daba ne sun kai hari wani masallaci da ke yankin Rigasa a Jihar Kaduna, inda suka kashe wani matashi yayin da ake tsaka da sallar Tahajjud.

Sai dai rundunar ’yan sandan jihar, sun kama mutum 12 da ake zargi da hannu a kai hari masallacin.

Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar Namibia An wawushe motar abinci ta Hukumar WFP a Borno

Kakakin rundunar, Mansir Hassan, ya ce ’yan daban sun fito daga unguwanni daban-daban kamar Malalin Gabas, Tudun Wada, Rafin Guza, da Unguwar Baduko.

Sun kai farmaki Masallacin Layin Bilya, titin Makwa a Rigasa da misalin ƙarfe 2 na dare yayin da masu mutane ke sallar Tahajjud.

Kafin jami’an tsaro su isa wajen, sun sun daɓa wa wani matashi mai shekara 28, Usman Mohammed, wuƙa har lahira.

Rundunar tare da haɗin gwiwar JTF sun ɗauki mataki cikin gaggawa, inda suka kama mutum 12 kuma ana bincike a kansu.

Haka kuma, an samu makamai a hannu waɗanda aka kama.

An fara bincike domin gano gaskiyar lamarin da tabbatar da cewa an hukunta waɗanda suka aikata laifin.

Sakamakon haka, ’yan sanda sun ƙara tsaurara matakan tsaro a wuraren ibada da sauran wuraren da ake ganin za su iya fuskantar barazana.

Hukumomi sun buƙaci al’umma da su kasance masu sanya ido tare da gaggauta kai rahoto idan sun ga wani abun zargi.

’Yan sanda sun kuma gargaɗi masu aikata laifi da su daina ko su fuskanci hukunci mai tsanani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gobara ta tashi a gidan mai sakamakon fashewar tanka a Neja
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara
  • Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi
  • Amurka ta cire tukuicin wanda ya bayar da bayani kan mataimakin shugaban Taliban
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [15]
  • Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho
  • GMBNI Ta Yi Allah-wadai Da Kisan Gillar Wani Almajiri A Jihar Jigawa
  • ’Yan daba sun hallaka matashi ana sallar Tahajjud a Kaduna
  • Gobara ta kashe ɗan shekara 7 a sansanin ’yan gudun hijira
  • Gobara Ta Kashe Yaro A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Maiduguri