‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja
Published: 9th, February 2025 GMT
“Da sauri jami’an ‘yansanda suka isa wurin, inda suka gano wata mata ‘yar shekara 25 mai suna Promise Eze, ‘yar Jihar Ebonyi, daure a wata karamar kujera an rufe bakinta da filasta. An same ta a sume kuma cikin damuwa. Jami’an ‘yan sanda sun dauki matakin gaggawa, inda suka kubutar da ita daga hannun wadanda aka yi garkuwa da su, sannan suka garzaya da ita asibitin gundumar Wuse, inda ta farfado,” in ji sanarwar.
Adeh ta ce binciken farko da aka yi ya nuna cewa Eze ta leka otal din a safiyar ranar 30 ga watan Janairu tare da Okoro, wanda ta hadu da shi ta intanet.
A cewarta, wanda ake zargin ya gabatar da kansa a matsayin ma’aikacin kamfanin mai da ke Jihar Delta.
Adeh ta bayyana cewa tun da farko wanda ake zargin ya gayyaci Eze ta ziyarce shi a Jihar Delta amma ta ki amincewa da hakan amma ta amince ta same shi a Abuja a maimakon haka.
“Bincike na farko ya nuna wani yanayi na yaudara da tashin hankali, ta shiga otal ne kwana daya da ta gabata, a ranar 30 ga watan Janairu, 2025, da misalin karfe 7:00 na safe, tare da wani mutum da ya bayyana sunansa da Emmanuel Okoro daga Jihar Legas.
“Sai dai yayin da ‘yansanda ke mata tambayoyi, matar da aka cutar ta bayyana cewa ta hadu da wanda ake zargin a intanet, inda ya gabatar da kansa ga Michael Prince, inda ya ce shi ma’aikacin kamfanin mai ne da ke Jihar Delta.”
Adeh ta kara da cewa Eze ya ce Okoro ya fid da wuka don yi mata barazana kafin ya daure ta ya manne bakinta a cikin bandakin otal din.
Adeh ta ce kwamishinan ‘yansandan Babban Birnin Tarayya Abuja, CP Olatunji Disu, ya yi Allah wadai da faruwar lamarin tare da shawartar ‘yanmata kan illar haduwa da baki ta intanet ba tare da taka tsantsan ba.
এছাড়াও পড়ুন:
Tsarin Fansho Na Jihar Jigawa Ya Yi Wa Sauran Jihohi Zarra- Premium Pension
Hukumar bayar da gudunmawar fansho ta Jihar Jigawa da Kananan Hukumomin jihar ta kulla yarjejeniyoyi da wasu mashahuran Hukumomin Asusun Fansho guda shida (PFA) da nufin tabbatar da tafiyar da kudaden fansho na jihar yadda ya kamata.
Shugaban ma’aikata na jiha Alhaji Muhammad K Dagaceri wanda ya jagoranci rattaba hannu kan yarjejeniyar a madadin gwamnatin jihar Jigawa a gidan fensho na Dutse ya ce taron yana kara jaddada kudirin gwamnati na tabbatar da gaskiya da inganci a tsarin tafiyar da fansho.
Ya kuma jaddada mahimmancin kula da harkokin kudi da kuma bukatar samar wa wadanda suka yi ritaya kudaden fansho domin ci gaba da gudanar da rayuwarsu.
“Wannan yarjejeniya ta nuna wani gagarumin ci gaba a kokarin da muke yi na ganin cewa ma’aikatanmu da suka yi ritaya sun samu haƙƙinsu a kan lokaci.”
Alhaji Muhammad Dagaceri ya ci gaba da bayyana cewa, an zabo shugabannin asusun fansho ne ta hanyar tantancewa.
A cewarsa, masu gudanar da ayyukan za su samar da ingantattun ayyukan gudanarwa, da suka hada da dabarun saka hannun jari, da kula da ayyukan asusu da inganta ayyukan abokan ciniki.
Shugaban Ma’aikatan ya ce Hukumar Fansho ta Jihar Jigawa za ta sa ido a kan hadakar, tare da tabbatar da cewa PFA sun bi ka’ida da kuma cika alkawuran da suka dauka ga Jihar da masu karbar fansho.
Ya jaddada sadaukarwar gwamnatin Gwamna Umar Namadi wajen kyautata jin dadin ma’aikatan da suka yi ritaya, yana mai cewa wannan wani bangare ne na kokarin inganta ayyukan gwamnati da kuma kaucewa rikon sakainar kashi a harkokin tafiyar da dukiyar jihar.
Da yake jawabi a madadin hukumomin na PFA Manajan Daraktan Asusun Fansho na Premium Hamisu Bala Idris, ya tabbatar wa hukumar cewa PFA da aka zaba za su ci gaba da aiki yadda ya kamata ta hanyar bin duk wasu sharuddan da ke cikin yarjejeniyar.
Hamisu, ya bayyana tsarin fansho na jihar Jigawa a matsayin wanda ya fi kowanne a fadin kasar nan.
A nasa jawabin, Shugaban Hukumar Fansho ta Jihar Jigawa da Kananan Hukumomi, Dokta Bilyaminu Shitu Aminu ya bayyana cewa, zababbun asusun fansho guda shida da za su kula da dukiyar hukumar su ne, Premium Pension Fund (Lead PFA), da PAL Pension, da GT Pension, da NLPC Pension, da Norrenberger Pension da Cruder.
Dakta Bilyaminu Shitu Aminu ya yabawa Gwamna Malam Umar Namadi bisa gagarumin goyon bayan da ya bayar ga shirin da ya sa Jihar ta zama abin koyi a kasar nan.
Usman Muhammad Zaria