HausaTv:
2025-04-22@00:34:10 GMT

Fizishkiyan: Kasashen Musulmi Za Su Iya Sake Gina Yankin Gaza

Published: 9th, February 2025 GMT

Shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya yi kira da a kafa kawancen duniya da dukkanin kasashen musulmi za su shiga ciki, domin taimakawa mutanen Gaza, da sake gina yanki, tare da cewa, kasashen musulmi kadai za su iya sake gina yankin na Gaza tare da dawo da rayuwa a cikinsa.

A ganawar da ya yi da mambobin majalisar jagoranci ta kungiyar Hamas, anan Tehran ya yi jinjina ga shahidan kawancen gwagwarmaya, ya kuma yi murna akan nasarar da ‘yan gwgawarmaya su ka samu akan ‘yan sahayoniya.

Shugaban kasar ta Iran ya kara da cewa; Nasarorin da mutanen na Gaza su ka samu, sun hana makiya ‘yan sahayoniya cimma manufofin da su ka shata, duk da cewa adadin shahidan da aka samu suna da yawa.

Haka nan kuma ya ce; Abinda ya faru, ya cancanci a yi jinjina a gare shi, tare da kuma da taya dukkanin mayaka da dukkanin mutanen Gaza murnar samun nasara.

A nasu gefen, ‘yan majalisar jagorancin na kungiyar Hamas, sun gode wa jamhuriyar Musulunci ta  Iran da dukkanin ‘yan gwgawarmaya, da kuma taya su murnar nasarar da aka samu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Cutar Da Ke Kassara Gonakin Tumatir Ta Sake Bulla A Jihar Kano

A cewarsa, hakan ya kuma jawo lalata gonakin na Tumatirin da ke wasu sassan jihar.

Yadakwari ya kara da cewa, hakan ya tilastawa manoman Tumatir da dama a jihar dakatar da nomansa, duba da irin mummunar asarar da suka yi.

Ya ci gaba da cewa, manoman Tumatir da suka fara lura da barkewar cutar ce suka sanar da kungiyar, inda kuma kungiyar ta shigo cikin lamarin ta kuma gano cewa, cutar ce ta sake dawowa gonakin manoman na Tumatir.

A cewarsa, maoman Tumatir a jihar, sun shafe shekaru suna yin asara sakamakon barkewar cutar, wanda hakan ya sanya wa manoman rashin sha’awar ci gaba da noman nasa.

“Mun gano bullar annobar ce a wasu gonakin da aka shuka Tumatir a

Garun Malam, Kura, Bunkure, Bagwai da sauransu”, in ji Yadakwari.

Ya sanar da cewa, duba da ilimin da muke da shi kan cutar, mun yi zargin cewa, annobar ce ta sake dawo ga gonakin na noman Tumatir da ke jihar.

“A bangaren kungiyar, mun dauki matakan da suka dace tare da rubuta wasika zuwa ga ma’aikatar aikin gona ta jihar, domin sanar da su dawowar annobar, inda a yanzu muke ci gaba da jiran amsa daga wurinsu”, a cewar Yadakwari.

Wannan cuta dai, an gano bullarta ne a shekarar 2016, wadda kuma ta jawo lalata gonakin manoma da dama da ke jihar.

Bugu da kari, bayan sake dawowar cutar, an fara fuskantar karancin Tumatir a akasarin kasuwannin da ke jhar, wanda kuma hakan ya haifar da tashin farashinsa zuwa sama da Naira 75.

Kazalika, manomansa da hukumomin gwamnati, sun tashi tsaye wajen yakar wannan cuta, amma sai dai, har yanzu kwalliya ba ta biya kudin sabulu ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gina Al’umma Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya: Jigon Ziyarar Xi A Kudu Maso Gabashin Asiya
  • Burnley Da Leeds United Sun Dawo Gasar Firimiya Lig 
  • Tsakanin Kafa Shingaye Da Gina Gada: Yadda Matakan Amurka Da Sin Suka Bambanta Sosai
  • Wasu Falasdinawa Sun Yi Shahada A Harin Sojojin Mamayar Isra’ila Kan Zirin Gaza
  • Iran Ta Yi Watsi Da Barazanar HKI
  • Zaɓen 2027: Babu ɗan takarar da zai yi nasara ba tare da goyon bayan Arewa ba — Hakeem
  • Har Yanzu Ruhin Taron Bandung Yana Tare Da Mu Wajen Kara Karya Lagon Babakere
  • Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97
  • Cutar Da Ke Kassara Gonakin Tumatir Ta Sake Bulla A Jihar Kano
  • Iran ta yi tir da kakkausar murya da harin Amurka kan tashar mai ta Yemen