Sam Nujoma Da Ya Samarwa Kasar Namibia ‘Yanci Ya Rasu Yana Dan Shekaru 95
Published: 9th, February 2025 GMT
Shugaban kasar Namibia dake kan gado Nangolo Mbumba ne ya sanar a yau Lahadi cewa, jagoran samun ‘yacin kasar Sam Nujoma ya rasu a jiya Asabar da dare, bayan da aka kwantar da shi a wani asibitin babban birnin kasar Windhoek.
Sanarwar da shugaban kasar ta Namibia mai ci a yanzu, ya fitar ya bayyana mutuwar Nujoma da cewa; ginshikin da aka kafa kasar akansa ya girgiza.
Sam Nujoma ya jagoranci fadan sama wa kasar ta Namibia ‘yanci daga mulkin nuna wariyar launin fata na Afirka ta kudu, a shekarar 1990, sannan kuma ya jagoranci kasar na tsawon shekaru 15.
A lokacin da yake a raye, al’ummar kasar ta Namibia suna girmama shi matuka a matsayin wanda ya jagoranci fadan samun ‘yanci sannan kuma ya dora kasar akan turbar demokradiyya.
A yayin gwagwarmayarsa ta nema wa kasar ‘yanci, Nujoma ya yi shekaru 30 yana gudun hijira. Kasar dai ta sami ‘yanci ne daga mulkin mallakar tsarin Wariya na Afirka ta Kudu a 1989, bayan da a baya ta kasance a karkashin mulkin mallakar jamus. Majalisar dokokin kasar ta zabe shi a matsayin shugaban kasa a 1990.
Nujoma ya kasance a sahu daya da jagororin da su ka yi fafutukar samun ‘yanci a nahiyar Afirka da su ka hada Nelson Mandela na Afirka Ta Kudu, Robert Mugabe na Zimbabwe, Kenneth Kaunda na Zambia, Julius Nyerer na Tanzania da Samora Machel na Mozambique.
Kungiyar neman ‘yanci ta SWAPO wacce Nujoma ya jagoranta ta dauki shekaru 20 tana fada da makamai, wacce kuma ta sami cikakken goyon baya a duniya daga ciki har da MDD.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Iran Ya Aike Da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Papa Roma Farancis
A yau Litinin shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya fitar da sanarwa ta nuna aljinin rasuwar Papa Roma Farancis,sannan kuma ya mika sakon ta’aziyya ga Mabiya darikar Roman Katolika na duniya.
Shugaban kasar ta Iran ya rubuta cewa; Daga cikin matsaya da ta kasance fitacciya wacce Papa Roman ya dauka a lokacin rayuwarsa ita ce ta kalubalantar yadda ake take hakkin bil’adama a duniya, musamman mai dai yadda ya yi Allawadai da kisan kiyashin da ‘yan sahayoniya suke yi wa Falasdinawa a Gaza. Haka nan kuma yadda ya rika yin kira da HKI ta kawo karshen kisan kiyashin da take yi, da kashe mata da kananan yara.
Fizishkiyan ya kuma kara da cewa; Wadannan matakan da Papa Roman ya dauka a lokacin rayuwarsa za su wanzar da ambatonsa a cikin zukatan masu rayayyen lamiri da kuma wadanda suke yin kira da tabbatr da ‘yanci a duniya.
Shugaban kasar na Iran ta kitse sakon nashi da cewa; A madadin ni kaina da kuma al’ummar Iran ina yin jinjina ga mamacin wanda ya yi fafutuka wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a duniya.
A yau Litinin ne dai Fadar Vatican ta sanar da rasuwar Papa Roma Farancis wanda shi ne dan asalin yankin Latin na farko da ya jagoranci majami’ar .
Fadar ta kuma sanar da zaman makoki na kwanaki 9, sannan kuma ta sanar da cewa nan da makwanni biyu zuwa uku za a fara shirye-shiryen zabar sabon Papa Roma.