OIC Ta Yi Allawadai Da Furucin Shugaban Kasar Amurka Akan Gaza
Published: 9th, February 2025 GMT
Kungiyar kasashen musulmi ( OIC) ta fitar da bayani da aciki ta yi tir da maganganun shugaban kasar Amurka Donald Trump akan fitar da mutanen Gaza.
Kungiyar ta OIC ta bayyana cewa; maganganun na shugaban kasar Amurka suna a matsayin goyon bayan ‘yan mamaya, masu mulkin mallaka domin kwace kasar Falasdinawa da hakan yake a matsayin take dokokin kasa da kasa da kudurorin MDD da su ka hada da kwamitin tsaro na wannan Majalisar mai lamba;2334.
Haka nan kuma bayanin na kungiyar kasashen musulmin ya ce, abinda Trump ya furta zai iya hana zaman lafiya wanzuwa a cikin wannan yankin.
Wani sashe na kungiyar kasashen musulmin ya bayyana kin amincewa da duk wani yunkuri na sauya tsarin iyaka da mutane a Falasdinu, tare da yin kira da a tsagaita wutar yaki mai dorewa.
Haka nan kuma kungiyar ta OIC ta nuna cikakken goyon bayanta ga hukumar Agaji ta Falasdinawa ta “UNRWA” wacce Isra’ila da Amurka su ka haramtawa kansu aiki da ita.
Kungiyar ta kuma nuna cikakken goyon bayanta ga al’ummar Falasdinu da kuma fadi tashin da suke yi na samun ‘yanci a karkashin kungiyar PLO.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Brice Ologui Ya Lashe Zaben Shugaban Kasar Gaban Da Kashi 90.35% A Jiya Lahadi
Shugaban gwamnatin rikon kwarya na kasar Gabon wanda kuma ya jagoranci juyin mulkin da aka yiwa Ali Bongo tsahon shugaban kasar ya lashe zaben da aka gudanar a jiya Lahadi tsakanin yan takara 7 har da shi.
Shafin yanar gizo na labarai ‘Africa News” ya bayyana cewa Oligui dan shekara 50 a duniya, shi ne babban dogarin sojoji masu tsare fadar shugaban kasar Gaban, a lokacinda ya jagoranci juyin mulkin da ya kawo karshen mulkin da yan gidan Bogo suka yi na shekaru kimani 50 a kasar.
Labarin ya kara da cewa kashi 2/3 na mutanen Gabon wadanda yawansu bai fi miliyon 2.3 ba suna cikin talauci a cikin kasa wacce take da arziki mai yawa.
Brice zai jagoranci kasar na tsawon shekaru 7 masu zuwa kuma yana iya sake shi takarar shugabancin kasa karo na biyu.
Yan takara 6 ne suka tsaya tare da Brice amma mai binsa bai sami fiye da kashi 3 % na kuri’un da aka kada ba sannan yawan fitowar mutane masu zabe ya kai kashi 70.4% wanda ya nuna cewa an sami sauyi babban a cikin harkokin siyasar kasar ta Gabaon.