Masar Ta Kirayi Taron Kasashen Larabawa Akan Makomar Falasdinu
Published: 9th, February 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Masar ta sanar da kiran taron kasahen larabawa a karshen wannan watan na Febrairu da ake ciki domin tattauna batun tilasta wa Falasdinawa yin hijira daga Gaza a karkashin shirin Amurka da Isra’ila.
Da safiyar yau Lahadi ne dai ma’aikatar harkokin wajen ta Masar ta bayyana cewa za ta karbi bakuncin taron kungiyar kasashen Larabawa a ranar 27 ga watan nan na Febrairu,domin tattauna sabbin batutuwan da su ka taso dangane da Falasdinu.
Har ila yau sanarwar ta ce, Masar din ta yi wannan gayyatar ne bayan tattaunawa da kasar Bahrain wacce a halin yanzu take rike da shugabancin kungiyar kasashen Larabawan, haka nan kuma tuntubar babbar shalkwatar kungiyar.
Bugu da kari Masar din ta sanar da cewa ta tuntunbi sauran kasashen larabawa da kuma gwamnatin Falasdinu, domin tattauna batutuwa masu hatsari da su ka bijiro akan batun Falasdinu.
A gefe daya, Masar din ta sanar da cewa, ministanta na harkokin waje Badar Abdul-Adhi, ya nufi kasar Amurka domin tattaunawa da mahukuntanta.
Shirin yin wannan taron na kungiyar kasashen larabawa ya zo ne bayan wani furuci da shugaban kasar Amurka ya yi na ganin Falasdinawa sun yi hijira daga Gaza, zuwa kasashen Masar da Jordan.
Donald Trump na Amurka ya bayyana aniyarsa ta yin manyan gine-gine a cikin zirin Gaza, bayan ficewar Falasdinawa da kuma karbar yankin da Amurka za ta yi daga hannun HKI.
Tuni dai shugaban na kasar Amurka ya fara fuskantar suka daga bangarori mabanbanta.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jakadan Sin Dake Najeriya Ya Gana Da Karamar Ministar Harkokin Wajen Kasar
Jakadan Sin dake kasar Najeriya Yu Dunhai ya gana da karamar ministar harkokin waje ta kasar Bianca Odumegu-Ojukwu.
Jakada Yu ya bayyana cewa, a shekarar bara, shugaban kasar Sin Xi Jinping da shugaban kasar Najeriya Bola Tinubu, sun sanar da inganta dangantakar dake tsakanin Sin da Najeriya zuwa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni, wanda ya zama babban ci gaba ga raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. A farkon shekarar bana kuma, memban hukumar kula da harkokin siyasa ta kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin kuma ministan harkokin wajen kasar Wang Yi ya kai ziyara Najeriya cikin nasara, hakan ya kara kyautata dangantakar dake tsakanin kasashen biyu zuwa sabon matsayi. A cewar jakadan, Sin tana son hada shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya da manufar fatan samun farfadowa ta Najeriya, da kara hadin gwiwa bisa manufofin raya kasashen biyu, da raya manufar makomar bai daya ta Sin da Najeriya mai inganci, yana mai cewa, ta hakan za su taka muhimmiyar rawa wajen sa kaimi ga hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa a duniya.
A nata bangare, madam Bianca Odumegu-Ojukwu ta bayyana cewa, shugaba Tinubu ya kai ziyara kasar Sin a shekarar bara, lamarin da ya shaida cewa, Najeriya tana maida hankali ga raya dangantakar dake tsakaninta da Sin. Ta ce kasar Najeriya ta tsaya tsayin daka kan manufar Sin daya tak, kuma tana son hada hannu da kasar Sin wajen aiwatar da ayyukan da aka cimma a ganawar shugabannin kasashen biyu da taron koli na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka na Beijing, ta yadda za a inganta hadin gwiwar kasashen biyu har ya amfanawa jama’arsu baki daya. (Zainab Zhang)