Iran Ce Kasa Ta 10 A Duniya Wajen Samar Da Wutar Lantarki
Published: 9th, February 2025 GMT
An bayyana cewa Iran ce kasar ta 10 a duniya wajen samar da wutar lantarki, da yawan megawati dubu 94 da 846.
Manajan da yake kula da tsara manyan ayyuka a ma’aikatar makamashi ta Iran, Behruz Muradi ya bayyana cewa, shekru 46 da su ka gabata, wato a lokacin juyin juya halin musulunci, yawan megawatin da Iran take samarwa ya yi kasa da wanda ake da shi a yanzu har sau hudu.
Manajan ya kuma kara da cewa wutar lantarki da ake da ita a Iran da karfin tsarin da take da shi, tana taka rawa mai muhimmanci wajen gina tattalin arzikin kasar. Haka nan kuma ya ce, da akwai kyakkyawan tsarin da ake da shi ya samar da cigaba a cikin bangarorin ruwan sha, da kuma noma da kiwo.
Behruz Muradi ya kuma ce, ci gaban da aka samu a fagen wutar lantarki a Iran yana daga cikin nasararon juyin juya halin musulunci.
Hanyoyin da Iran take samar da wutar lantarki, sun hada da madatsun ruwa, iska, hasken rana da kuma wasu sabbin hanyoyin na zamani.
Dangane da yawan garuruwan da suke da wutar lantarki a Iran, manaja Muradi ya ce, A halin yanzu da akwai kauyuka da sun kai 58,000, da 829 da suke da wutar lantarki.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: da wutar lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Arakci: Babu Wanda Zai Yi Tunanin Kawo Wa Iran Hari
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa; Iran tana cikin shirin ko-ta-kwana akan duk wani abu da zai iya bijirowa, kuma a halin yanzu ba batun yaki ake yi ba.
A wata ganawa da ministan harkokin wajen na Iran ya yi da tawagar kungiyar agaji ta “Red Cross” a karkashin jagorancin shugabanta Koliband, ministan harkokin wajen na Iran ya yabawa aikin nasu, tare da cewa; Duk da cewa ana cikin lokacin hutu, amma su a kodayaushe suna cikin shirin ko-ta-kwana domin gabatar da ayyukan agaji da hakan yake nuni da yi wa al’umma hidima ta koli.
Ministan harkokin wajen na Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci ya kuma ce: Su ma sojoji da jami’an tsaro kamar ku suke aiki, ba su da lokacin hutu,kodayaushe suna cikin shirin ko-ta-kwana.
Haka nan kuma ya kara da cewa; Kowane bangare na gwamnati yana cikin shirin ko-ta-kwana domin fuskantar kowane irin yanayi.
Har ila yau, babban jami’in diflomasiyyar ta Iran ya ce; Ina da tabbacin cewa babu wani mahaluki da yake tunanin kawo wa Iran hari, domin suna sane da sakamakon da take tattare da yin hakan, sun kuma san cewa kowane bangare na gwamnati yana cikin shiri.
Abbas Arakci ya kuma bayyana cewa baya ga ayyukan agaji da kungiyar take yi a cikin gida, tana kuma gabatar da wasu ayyukan na taimako a kasashen waje. Ya kuma yi ishara da lokacin girgizar kasar Japan, da hukumar agaji ta Iran ta kai dauki, wanda ya taka rawa wajen kara bunkasa alaka a tsakanin kasashen biyu.