Aminiya:
2025-03-25@09:52:41 GMT

Ɗan sanda ya rataye kansa har lahira a Neja

Published: 9th, February 2025 GMT

Wani Mataimakin Sufeton ’Yan Sanda (ASP), Shafi’u Bawa, da ke aiki da Rundunar 61 Police Mobile Force a Kontagora da ke Jihar Neja, ya hallaka kansa har lahira.

Wani jami’in dan sanda ya shaida wa Aminiya cewa, lamarin ya faru ne a ranar Asabar.

Gwamnatin Kano ta dakatar da wani fim mai suna Zarmalulu Aisha Binani ce ta lashe zaɓen Adamawa, ina da ƙwararan hujjoji – Ari

An tsinci gawarsa rataye a cikin dakinsa.

Majiyoyi sun ce mahaifinsa, Malam Usman Bawa ne, ya fara gano abin da ya faru sannan ya kai rahoton lamarin zuwa ofishin ’yan sanda da ke Kontagora.

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce: “A ranar 8 ga watan Fabrairu, 2025, da misalin karfe 2 na rana, an samu rahoton cewa ASP Shafi’u Bawa na Rundunar 61 PMF, Kontagora, ya rataye kansa.

“Har yanzu ba a san dalilin da ya sa ya aikata hakan ba.

“An dauke gawarsa tare da mika ta ga iyalansa domin yi mata jana’iza.

“Ana ci gaba da bincike don gano musabbabin faruwar lamarin.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rataye Kai

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila ta kashe wani mamba na ofishin siyasa na Hamas

Wani sabon kazamin harin sojojin Isra’ila ya yi sanadin shahadar mutum 40 cikin sa’o’I 24 da suka gabata ciki har da Salah al-Bardawil, dan majalisar Falasdinu kuma mamba a ofishin siyasa na kungiyar gwagwarmaya ta Hamas.

A cikin wata sanarwa da ta fitar yau, Hamas ta ce an kai wa Bardawil hari ne a wani hari na ” yahudawan sahyoniya na ha’inci”, a lokacin da yake gudanar da sallar dare a daren 23 ga watan Ramadan.

An kashe shi ne tare da matarsa ​​a wani hari da Isra’ila ta kai ta sama a kan tantinsa da ke yankin al-Mawasi, yammacin birnin Khan Yunis na kudancin Gaza.

Kungiyar ta bayyana Bardawil a matsayin “alama ta siyasa, yada labarai,” da ayyukan bunkasa al’umma da yankin Falastinu.

Isra’ila ta kaddamar da yakin kisan kare dangi a Gaza a ranar 7 ga Oktoba, 2023, amma ta kasa cimma manufofinta duk da kashe Falasdinawa 49,747, galibi mata da kananan yara, tare da jikkata wasu fiye da 113,213 a yankin da aka yi wa kawanya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ukraine: Tawagogin Rasha da Amurka sun kammala tattaunawa a Saudiyya
  • Isra’ila ta kashe Falasdinawa 61 cikin sa’o’i 24
  • Fursunoni 12 sun tsere bayan fasa gidan yari a Kogi
  • Ƴansandan Sun Gayyaci Sanata Karimi Kan Zargin Shigar Kungiyar Leƙen Asirin Rasha Majalisa’
  • Gobara ta tashi a gidan mai sakamakon fashewar tanka a Neja
  • Iran Tace Zata Kaddamar Da Sabbin Magunguna Da Ta Samar Tare Da Amfani Da Makamashin Nukliya
  • Isra’ila ta kashe wani mamba na ofishin siyasa na Hamas
  • Gwamnatin Kano Ga Ma’aikata: Duk Mai Bukatar Aikinsa Dole Ya Gabatar Da Kansa A Wajen Tantancewa
  • Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027
  • Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho