Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na sharhin bayan labarai, wanda zai yi magana a kan “Yadda JMI Ta Bunkasa Sana’argine-gine da da kamfanoni tare da amfani da fasahar cikin gida’ wanda ni tahir amin zan karanta.

Tun bayan nasarar juyin juya halin musulunci a nan kasar Iran a shekara 1979, daya daga cikin bangarorin da aka sami gagarumin ci gaba a cikinsa shi ne, bunkasa sana’ar gine –gine da kuma samar da masana’antu, wanda ya kai ga kasar ta kai ga wadata a wannan bangaren, wani abu daga kasashen waje, sai abunda ba za’a rasaba.

Har’ila yau wannan ya wadanar da mutane da dama a kasar.

Kafin haka idan mun dubi kasar Iran kafin juyin juya halin musulunci a kasar, zamu ga cewa kusan duk wani al-amari ya shafi gine-gine na hanya gadoji asbito ci, da gidaje . Haka ma masana’antu sun dogara kacokap kan kasashen waje musamman Amurka.

A cikin rabin karni na 20TH bayan an sami arzikin man fetur a kasar Iran, ci bayan da kasar ta yi ya sa da dogara da kasashen waje musamman Amurka do samar da hanyoyi da layukan dogo da gadaje da madatsun ruwa da gine-ginen zamani a manya manyan biranen kasar. Muna iya cewa dukkan manya-manyan ayyuka kamfanonin kasashen waje ne suke gana su, ba’abinda ira niyawa zasu iya yi sai ayyukan karfi da wasu wadanda basu da muhimmanci sosai.

A tsakanin shekara 1960-70, kamfanonin Amurka ne suka mamaye mafi yawan ayyukan ginegine a kasar Iran. Sannan a lokacin yakin cacan baki Amurka ce da mamaye dukkan harkokin tsaron kasar Iran. Da kuma kamfanonin haka da sarrafa man fetur.

A lokacinda farashin danyen man fetur ya tashi Amurka ta yi kokarin ginin dukkan kudaden sun koma kasar Amurka. Barin talakawan Iran hannu banza, duk tare da kudaden da suka shiga hannun gwamnatin kasar.

Abubuwan da kwararru na cikin gida suka yi ya kara fallasa barnan da kamfanonin kasashen waje suka yi a kasar. Sannan takunkuman Amurka sun sanya wasu ayyukan ma gaba daya an daina su sabo kayakin aikin daga waje ake zuwa da su.

Don haka a cikin wannan halin kwararru na cikin gida suna kammala rukunin gidaje na Ecbatona a birnin Tehran wanda wani kamfanin amurka ya fara ginashi bai kare ba aka yi juyin juya hali ya bar aikin rabi da rabi.

Sannan bayan yaki na shekaru 8 gwamnatin Rafsanaja ta samar da shirin sake gina kasar wanda ya kawo sauyi mai yawa a bangaren gine-gine a ko wani bangaren a kasar. Wadanda suka hada da manya-manyan tituna rukunan gidaje, layukan dogo sabbin tasoshin jiragen sama da jiragen ruwa, madatsun ruwa da kayakin lantarku da sauransu.

Daga cikin matakan da sabuwar gwamnatin JMI ta dauka don warware matsalilin gidaje, a iran. Akwai basusuka masu sauki, kula da farashin kayaki, da rage farashin wasu kayaki musamman abinda don talaka ya samu, sannan rarraba filaye don gina gidaje da farashin mai rahusa.

Kodaitar da manya-manyan kamfanoni su karfafa kananan kamfanoni, ko daddaikun mutane da sauransu.

An yada shi’arin cewa , al-amuran kasar Iran ba zai sake komawa cikin hannun yan waje ba,.

Tare da wannan sai kamfanonin cikin gida suka kammala manya manyan ayyuka wadanda kamfanonin kasashen waje suka fara yi, basu karasa ba, sai suka fara sabbin gine-gine, wadanda suka sauya fuskar biranen Iran musamman a birnin Tehran.

Shekaru 46 da suka gabata, mafi yawan kasar Iran kauyuka ne, mafi yawan mutane suna rayuwa a kauyuka, amma a halin mafi yawan kasar Iran rayuwar birane suke, wanda ya tashi daga kashi 48 zuwa 77 %.

Daga lokaci zuwa yanzun an samar da birane kimani 1,300, daga 373 kacal kafin nasarar Juyin juya halin musulunci.

Kuma ana amfani da kayakin gini masu karfi ganin kasar tana fama da yawan girgizan kasa. Don haka a halin yanzu girgizan kasa mai ma’auninriche 5-7 ba zasu yi barna mai yawa ba, saboda ingancin gine gine.

Banda wannan Iran ta kai matsayinda a wasu bangarori ta shiga cikin kasashe 10 masu samar da misali ceminta da karafa a duniya. Sannan tana sayar da su ga kasashen waje. A bangare kayakin kawa sai kasar Chaina da indiya ce suke gabanta. Masu sauraro karshen sharhin bayan labaran Kenan.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a manya manyan kasashen waje

এছাড়াও পড়ুন:

Dagewa Iran Takunkuman Zalunci Na Daga Cikin Manufofin Tattaunawa Da Amurka: Aref

Matainakin shugaban kasar kasar Iran na farko Mohammad Reza Aref ya bayyana cewa, daukewa Iran takunkuman zalunci wadanda kasashen yamma suka dora mata na daga cikin asalin hakkin kasar da aka tauye.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Aref yana fadar haka a jiya Asabar, ya kuma kara da cewa, kasar Iran ba zata manta da hakkin kasar wanda Amurka ta take tun farkon nasarar juyin juya halin kasar shekaru 46 zuwa yanzu ba, amma duk da haka sun bata damar tattaunawa.  Yace: Muna son mu nunawa duniya kan cewa har yanzun muna hakuri, amma ba zamu taba manta da zaluncin da aka yi mana ba.   Mataimakin shugaban yana maganar ficewar kasar Amurka daga yarjeniyar JCPOA da kuma dorawa kasar takunkuman tattalin arziki mafi muni da nufin kifar da gwamnatin kasar. Yace dukkan takunkuman tattalin arzikin da gwamnatocin kasar Amurka ta dorawa kasar tun bayan nasarar juyin juya halin kasar shekaru 46 da suka gabata basa bisa ka’ida.  Mataimakin shugaban kasar yana fadar haka ne bayan da ministan harkokin wajen kasar Abbas Aragchi ya kammala zagaye na farko na tattaunawa ba kai tsaye ba kan shirin makamacin Nukliya na kasar da tokwaransa na kasar Amurka Steve Witkoff a kasar Omman tare da ministan harkokin wajen kasar Omman Badr Hamad Al-Busaidi a matsayin mai shiga tsakani.

Iran Ta Godewa Omman Da Shiryawa Da Kuma Gudanar Da Tattaunawa  Tsakanin Amurka Da Iran

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Jiragen Saman Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Luguden Wuta Kan Asibitin Baptist Da Ke Gaza
  • Amurka ta janye harajin kayan laturoni da ake shiga da su ƙasar
  • Dagewa Iran Takunkuman Zalunci Na Daga Cikin Manufofin Tattaunawa Da Amurka: Aref
  • Ukraine na Fuskantar Wata Barazana, Dangane Da Bukatar Amurka Na Kwace Iko Da Cibiyar Gas Na Rasha  A cikin Kasar
  • Amnesty Ta Zargi  Rundunar “RSF” Ta Sudan Da Cin Zarafin Mata
  • Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo
  •  A Yau Asabar Ne Ake Bude Tattaunawa A Kasar Oman Akan Shirin Makamashin Nukiliyar Iran
  • Saudiya Tace Shigo Da Agaji Cikin Gaza Bai Da Dangantaka Da Tsagaita Wuta
  • Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu