An bude atisayen soja kan teku bisa hadin gwiwar wasu kasashe a birnin Karachi na kasar Pakistan, a ranar 7 ga wata.

Asitayen sojan da kasar Pakistan ta tsara ya samu halartar jiragen ruwan soja daga kasashe sama da guda 10, wadanda suka hada da Sin, da Indonesiya, da Japan, da Italiya, da Malasiya, da kuma Amurka da dai sauransu.

Haka kuma, sauran kasashe sama da guda 40 sun tura masu sa ido wajen atisayen.

An raba atisayen sojan zuwa matakai guda biyu. Mataki na farko shi ne tsakanin ranaku 7 zuwa 9 ga watan Fabrairu, inda za a yi atisayen soja kan tashar jiragen ruwa, da tattaunawa kan atisayen, da tattaunawa kan ayyukan musamman tsakanin bangarori daban daban da dai sauran ayyuka. Sa’an nan, a tsakanin ranaku 10 zuwa 11 ga watan Fabrairu, za a fara mataki na gaba, wato atisayen soja kan teku, inda za a gudanar da atisaye a kan teku, da aikin binciken jiragen ruwan soja na kasa da kasa. Kana, mahalartar atisayen za su gudanar da ayyukan samar da kayayyaki da abubuwan da sojojin ruwa ke bukata, da kuma hadin gwiwa wajen yaki da ‘yan fashin teku da dai sauran ayyuka. (Mai Fassara: Maryam Yang)

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: atisayen soja kan

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ce Kasar Wacce Ta Fi Shigar Da Kayakin Kasuwanci Zuwa Kasar Afganistan A Shekarar Da Ta Gabata

Ma’aikatar kasuwanci ta kasar Afganistan ta bada sanarwan cewa kasar Iran ce a gaba da dukkan kasashen makobta da kasar Afganisatan wacce tafi shigo da kayakinta cikin kasar a shekara ta 1403 ta kalandar Iraniyawa da ta kare.

Kamfanin dillancin labaran Parstoday na kasar Iran ya nakalto kakakin ma’aikatar kasuwanci ta kasar Afganistan Abdussalam Jawad Okhande-Zadeh ya na fadar haka a yau Lahadi:

Ya kuma kara da cewa, kasashen da suka shigo da kayaki a kasar Afganistan a shekarar da ta gabata sun hada ta Iran, a gaba da ko wace kasa, sannan Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), Pakisatn, China da kuma Turkamanistan.

Kakakin ma’aikatar kasuwancin ta kasar Afganisatn ya ce a dayan bangaren kuma kasar Afaganista ta fidda kayaki zuwa kasashen waje wadanda kimarsu ya kai dalar Amurka biliyon guda a shekarar da ta gabata, kuma sun hada da busassun yayan itace, da darduma, da awduga da duwatsu masu daraja.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Lafiya Ya Yi Alƙawarin Inganta Tallafi Ga Likitoci A Hajjin 2025
  • Kiyaye Ci Gaba Mai Dorewa A Huldar Sin Da Amurka Ya Dace Da Moriyar Sasssan Biyu
  •  Syria: Isra’ila Ta Kai Hari A Kan Sansanin Soja A Yankin Dar’a
  • Gwamna Uba Sani Ya Nada Sarkin Kauru Amirul Hajj Na Shekarar 2025
  • Wajibcin Gina Al’ummar Duniya Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya
  • Iran ta yi gargadin cewa keta hurumin Lebanon da Isra’ila ke yi barazana ne ga zaman lafiyar duniya
  • Iran Tace Zata Kaddamar Da Sabbin Magunguna Da Ta Samar Tare Da Amfani Da Makamashin Nukliya
  • Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya
  • Iran Ce Kasar Wacce Ta Fi Shigar Da Kayakin Kasuwanci Zuwa Kasar Afganistan A Shekarar Da Ta Gabata
  • EFCC Ta Cafke Mutum 21 Bisa Zarginsu Da Zambar Intanet A Bauchi