Aminiya:
2025-04-14@18:21:58 GMT

2027: Kwankwaso da Aregbesola sun gana kan makomar siyasar Najeriya

Published: 9th, February 2025 GMT

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya gana da tsohon ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola, a birnin Legas.

Kwankwaso ya bayyana a shafinsa na X cewa sun tattauna kan batutuwan da suka shafi siyasa da makomar dimokuradiyya a Najeriya.

Aisha Binani ce ta lashe zaɓen Adamawa, ina da ƙwararan hujjoji – Ari Ɗan sanda ya rataye kansa har lahira a Neja

Wannan ganawa na zuwa ne a daidai lokacin da jam’iyyun adawa ke kira ga haɗin kai domin fuskantar zaɓen 2027.

A watan Oktoban 2024, jam’iyyar APC a Jihar Osun ya dakatar da Aregbesola bisa zargin cin amanar jam’iyya da sukar shugabannin jam’iyyar, ciki har da Shugaba Bola Tinubu da tsohon gwamnan Osun, Bisi Akande.

Aregbesola, wanda ya kasance gwamnan Osun daga 2010 zuwa 2018, ya fuskanci rikici da magajinsa, Adegboyega Oyetola, tun bayan zaɓen 2018.

Wannan rikici ya haifar da rabuwar kai a cikin jam’iyyar APC a Osun, inda wasu magoya bayan Aregbesola suka kafa ƙungiyar Omoluabi Progressives, wanda jam’iyyar ta yi zargin cewa tana aiki ne a matsayin waniɓangare mai adawa da ita.

Duk da waɗannan ƙalubale, Aregbesola ya ci gaba da kasancewa mai faɗa a ji a siyasar Najeriya.

Ganawarsa da Kwankwaso na iya nuna yunƙurin ƙulla sabbin alaƙa da haɗin gwiwa tsakanin shugabannin siyasar domin inganta dimokuradiyya a Najeriya.

Har zuwa yanzu, ba a samu cikakken bayani kan abin da suka tattauna ba, amma ganawar ba za ta rasa nasaba da yunƙurin da wasu ke yi na haɗa kan ’yan adawa domin tunkarar babban zaben 2027.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Aregbesola dimokuradiyya Ganawa Kwankwaso Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Zulum Ya Gana Da Yaron Da Aka Ci Zarafi, Ya Ba Shi Gida, Tallafin Karatu

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Gana Da To Lam Na Vietnam
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno
  • Zulum Ya Gana Da Yaron Da Aka Ci Zarafi, Ya Ba Shi Gida, Tallafin Karatu
  • A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi
  • Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu
  • ’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa
  • Yaya ‘Yan Siyasar Amurka Ke Kasafta Harajin Ramuwar Gayya?
  • Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba —Ganduje
  • Axios: Makomar Tsarin Jarin Hujja A Duniya  Tana Girgiza