2027: Kwankwaso da Aregbesola sun gana kan makomar siyasar Najeriya
Published: 9th, February 2025 GMT
Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya gana da tsohon ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola, a birnin Legas.
Kwankwaso ya bayyana a shafinsa na X cewa sun tattauna kan batutuwan da suka shafi siyasa da makomar dimokuradiyya a Najeriya.
Aisha Binani ce ta lashe zaɓen Adamawa, ina da ƙwararan hujjoji – Ari Ɗan sanda ya rataye kansa har lahira a NejaWannan ganawa na zuwa ne a daidai lokacin da jam’iyyun adawa ke kira ga haɗin kai domin fuskantar zaɓen 2027.
A watan Oktoban 2024, jam’iyyar APC a Jihar Osun ya dakatar da Aregbesola bisa zargin cin amanar jam’iyya da sukar shugabannin jam’iyyar, ciki har da Shugaba Bola Tinubu da tsohon gwamnan Osun, Bisi Akande.
Aregbesola, wanda ya kasance gwamnan Osun daga 2010 zuwa 2018, ya fuskanci rikici da magajinsa, Adegboyega Oyetola, tun bayan zaɓen 2018.
Wannan rikici ya haifar da rabuwar kai a cikin jam’iyyar APC a Osun, inda wasu magoya bayan Aregbesola suka kafa ƙungiyar Omoluabi Progressives, wanda jam’iyyar ta yi zargin cewa tana aiki ne a matsayin waniɓangare mai adawa da ita.
Duk da waɗannan ƙalubale, Aregbesola ya ci gaba da kasancewa mai faɗa a ji a siyasar Najeriya.
Ganawarsa da Kwankwaso na iya nuna yunƙurin ƙulla sabbin alaƙa da haɗin gwiwa tsakanin shugabannin siyasar domin inganta dimokuradiyya a Najeriya.
Har zuwa yanzu, ba a samu cikakken bayani kan abin da suka tattauna ba, amma ganawar ba za ta rasa nasaba da yunƙurin da wasu ke yi na haɗa kan ’yan adawa domin tunkarar babban zaben 2027.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Aregbesola dimokuradiyya Ganawa Kwankwaso Siyasa
এছাড়াও পড়ুন:
Turkiya:Fiye Da’Yan Adawa 300,000 Su Ka Yi Zanga-Zanga Nuna Kin Jinin Tayyib Ordugan
KAmfanin dillancin labarun “al-Somariyya Newas” ya ambato jagoran ‘yan hamayyar siyasa na kasar Turkiya Uzgor Auzal yana fadin cewa: A daren jiya juma’a adadin wadanda su ka fito Zanga-zangar nuna kin jinin shugaba Rajab Tayyib Urdugan sakamakon sauke da kama ‘yan hamayyar siyasa da ya yi kaga kan mukamansu da su ka hada da magajin garin birnin Istanbul.
Magajin garin Istanbul Imam Uglu ya yi watsi da duk wata tuhuma da aa yi masa ta hannu a cin hanci da rashawa.
Kamfanin dillancin labaran “Reusters” ya nakalto wata majiyar shari’a tana cewa Imam Uglu ya yi watsi da dukkanin thume-tuhumen da aka yi masa masu alaka a cin hanci da rashawa.
Shi dai Imam Uglu zai tsaya takarar shugabancin kasa da Urdugan, kuma ana tsinkayo cewa zai iya lashe zabe.
Jami’ar adawa da Imam Uglu ya fito daga cikinta “ Turkish Republican Party” ta yi Allawadai da kama Imam Uglu, tare da bayyana shi da cewa, bi ta da kulli ne na siyasa kawai.
Bayan kama Imam Uuglu Zanga-zanga ta barke a cikin birane da garuruwa mabanbanta na kasar ta Turkiya tare da yin tir da abinda ya faru.