Bugu da kari, jami’in ya ce Sin na taimakawa Masar wajen kafa masana’antar samar da ababen hawa a cikin gida, ta hanyar kafa irin wadannan masana’atu a kasar. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Rangadi A Karamar Hukumar Jahun

Kwamatin lura da kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawa ya kaddamar da rangadi na yini biyu a karamar hukumar Jahun, domin tantance kwazon karamar hukumar ta fuskar gudanar da ayyukan raya kasa da sha’anin mulki da kashe kudade.

Shugaban kwamatin kuma wakilin mazabar Gwiwa, Alhaji Aminu Zakari, ya ce ziyarar na daga cikin ayyukan majalisa da suka hada da duba kasafin kudi da yin doka da kuma tantance abubuwan da gwamnati ta ke gudanarwa kamar yadda tsarin mulki ya tanadar.

Ya ce a lokacin wannan ziyara, kwamatin zai tantance kundin bayanan ayyukan raya kasa da rahoton zangon shekara da bayanan tarukan kwamatin tsaro da na gudanarwa.

Ya ce kwanitin zai kuma tantance bayanan ayyukan majalisar kansiloli da kuma alkaluman tattara kudaden shiga da takardun biyan kudade wato voucher daga watan October na 2024 kawo yanzu.

Alhaji Aminu Zakari ya kara da cewar, irin wannan ziyara tana bada damar ganawa gaba da gaba tsakanin bangaren majalisa da mahukuntan karamar hukuma da kuma kansiloli, dan musayen bayanai tare da bada shawarwari domin tabbatar da shugabanci nagari a matakin kananan hukumomi.

Tun farko a jawabinsa na maraba, Shugaban karamar hukumar Jahun, Alhaji Jamilu Muhammad Danmalam, ya lura cewa mu’amalarsa ta farko da ‘yan majalisa lokacin tantance kiyasin kasafin kudin 2024 ta ba shi damar samun Ilimi akan sha’anin milki, wanda hakan zai taimaka masa wajen jagorantar karamar hukumarsa cikin sauki.

Malam Jamilu Danmalam ya yi addu’a bisa fatan cewa ziyarar kwamatin za ta yi tasiri wajen inganta harkokin karamar hukumar da kuma al’ummar Jahun baki daya.

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Rangadi A Karamar Hukumar Jahun
  • Jihar Kano Ta Samar Da Wani Salo Na Bunkasa Ilmin Addinin Musulunci A Jihar
  • Yawan Kamfanonin Da Aka Kafa Da Jarin Waje A Sin Ya Zarace Miliyan 1.23
  • An Jinjinawa Kwarewar Sin A Bikin Nune-Nunen Ayyukan Gona Na Cote d’Ivoire
  • Gwamnatin Kano Ta Amince da  Kashe Naira Biliyan 33.4 Don Ayyukan Ci Gaba
  • Sin Ta Tabbatar Da Goyon Bayanta Ga Kafa Kasashe Biyu Ga Isra’ila Da Palasdinu
  • Juyin-juya-halin Kyautata Muhalli: Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Samar Da Makoma Mai Kyau
  • Abba ya sanya hannu kan dokar kafa rundunar tsaro ta Kano
  • Abba ya sanya hannu kan dokar kafa rundunar tsaro a Kano
  • Jaridar Maariv Ta Isra’ila Ta Bayyana Wasu Daga Cikin Hasarorin Da Yakin Gaza Ya Janyo Wa Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya