NAJERIYA A YAU: Shin Har Yanzu Akwai Masu Rufin Asiri A Najeriya?
Published: 10th, February 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Akan karkasa mutane gida-gida a bisa mizanin tattalin arziki, musamman a tsarin jari-hujja, inda ke da mawadata da kuma matalauta.
A tsakanin al’umma kuma akwai ajin mutane masu matsakaicin samu waɗanda ake kira “Middle Class”.
Akan sanya mutane a wannan aji ne galibi bisa la’akari da aiki ko sana’ar da suke yi, da kuɗin da suke samu, da matakin ilimin da suka kai, da ma matsayinsu a tsakanin al’umma.
Sai dai a baya-bayan nan irin wadannan muntane sun bi sahun matalauta wajen korafi game da yadda suke dandana kudarsu saboda tsadar rayuwa.
NAJERIYA A YAU: Dalilin Faɗuwar Farashin Tumatur A Kasuwa DAGA LARABA: Yadda Al’adun Aure A Ƙasar Hausa Suka Koma ‘Event Centre’Shin a iya cewa har yanzu akwai wannan aji na mutane a Najeriya ke nan?
Wannan ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Najeriya Tattalin Arziki
এছাড়াও পড়ুন:
Araqchi: Har yanzu Iran ba ta mayar da amsa ga wasikar Trump kan tattaunawar nukiliya ba
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya sanar da cewa har yanzu Iran ba ta mayar da martani kan wasikar da shugaban Amurka Donald Trump ya aike kan shirin nukiliyar Iran ba. Sai dai ya ce ana shirin mayar da amsa kuma za a mika ta hanyoyin da suka dace nan ba da jimawa ba.
Da yake magana a wani taron manema labarai na hadin gwiwa tare da ministan harkokin wajen Armeniya Ararat Mirzoyan a Yerevan, Araghchi ya nanata cewa Iran ba za ta shiga tattaunawa kai tsaye da Amurka ba a karkashin yanayin matsin lamba da barazanar soji, da kuma kakaba takunkumi.
Sai dai kuma ya tabbatar da cewa har yanzu ana ci gaba da tattaunawa da kasashen Turai uku, tare da tabbatar da aniyar Iran ta fuskar diflomasiyya.
Wasikar wadda Trump ya sanar da aikewa da ita a ranar 7 ga Maris, an aike da ita ne zuwa ga jagoran juyin juya halin muslunci na Iran Ayatullah Sayyed Ali Khamenei, a daidai lokacin da gwamnatin Amurka ke ci gaba da aiwatar da matakai na matsin lamba a kan Iran, a daya bangaren kuma take nuna sha’awar yin shawarwari tare da kasar ta Iran.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran Esmaeil Baqaei ya fayyace cewa Tehran ba ta da wani shiri na bayyana wasikar a bainar jama’a, yana mai cewa ba lallai bane jita-jitar da kafafen yada labarai suka yada a game da wasikar ya zama gaskiya.
Za a yi martanin ne game da wannan wasiku ta hanyoyin diflomasiyya bayan yin cikakken nazari a kai, in ji shi.