’Yan sanda na neman ’yan bola-jari ruwa a jallo a Abuja
Published: 10th, February 2025 GMT
’Yan sanda a Babban Birnin Tarayya Abuja sun buƙaci al’umma su kawo musu rahoton duk wanda aka ga yana sana’ar bola-jari a cikin gari.
Kwamishinan ’Yan Sanda na Abuja, Disu Olatunji, ne ya sanar da haka bayan taron Majalisar Tsaro ta Babban Birnin Tarayya wanda Minista Ezenwo Nyesom Wike ya jagoranta.
Idan ba a manta ba, a ranar 13 ga watan Janairu, 2025 ne Hukumar Babban Birnin Tarayya ta haramta ayyukan ’yan bola-jari a cikin faɗin birnin.
Umarnin ya taƙaita ayyukansu ga kan juji da ke ya yankunan da suke wajen birnin.
A lokacin zaman ne aka dakatar da ayyukan ’yan gwangwan na tsawon makonni biyu, saboda zargin alaƙarsu da ’yan bola-jari.
NAJERIYA A YAU: Shin Har Yanzu Akwai Masu Rufin Asiri A Najeriya? Ɗan sanda ya rataye kansa har lahira a NejaAn iya tuna cewa wannan lamari ya samo asali ne daga sace-sace kusan ɗauƙacin ƙarafunan murafen ramukan da ke kan titunan biran, waɗanda ake zargin ’yan bola-jari ne ke yi.
A yayin bincike da samame da aka kai a kasuwannin a sassan Abuja, jami’an tsaro sun gano ƙarafunan da wasu kayan gwamnati kamar fitilun kan titi da manyan wayoyin lantarki da sauransu a wurin wasu ’yan gwangwan.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Bola Jari Gwangwan yan bola jari
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya
Wani babban jami’in Diblomasiyya na kasar Iran ya bada sanarwan cewa zagaye na biyu a tattaunawa ba kai tsaye ba tsakanin JMI da Amurka za’a gudanar da shi ne a kasashen Turai a ranar 19 ga watan Afrilun wannan shekara ta 2025.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto mataimakin ministan harkokin waje na JMI kan al-amuran da suka shafi siysa Majid Takht-Ravabchi yana fadar haka a jiya Lahadi a lokacinda yake gabatarwa Majalisar dokokin kasar Iran rahoto kan taron tawagar Amurka da kuma JMI a birnin Mascat na kasar Omman a ranar Asabar da ta gabata.
Jami’in diblomasiyyar ya kara da cewa, a tattaunawar da ba kai tsaye ba tsakanin kasashen biyu a ranar Asabar da ta gabata yayin kokarin gano, wuri guda wanda zasu iya tsayawa a kansa don gina tattaunawar a kansa. Takht-Ravanchi ya nakalto tawagar gwamnatin Amurka na cewa da gaske suke a tattaunawar, kuma basa neman yaki da kasar Iran, banda haka a shirye suke su saurari korafe korafe gwamnatin JMI. A ranar Asabar da ta gabace ministan harkokin wajen kasar Amurka da wakilin kasar Amurka a harkokin gabas ta tsakiya Steve Witkoff suka gudanar da zagaye na farko a tsakanin kasashen biyu a birnin Mascat na kasar Omman. Tashar talabijin ta Al-Manar ta kasar Lebanon ta nakalto shafin yanar gizo na larabarai na Axion na fadar cewa taro nag aba zai kasance a birni Roma na kasar Italiya.