Ɗan fashi ya yi wa ɗaliban jami’a uku fyaɗe
Published: 10th, February 2025 GMT
Kotu ta tsare wani ɗan fashi da ya yi wa ɗalibai mata uku na Jami’ar Jihar Kwara fyaɗe.
Matashin da dubunsa ta cika yi wa ɗaliban fyade ne a yayin wani fashi a ɗakunan kwanan ɗalibai mata a cikin dare.
Ya yi musu wannan aika-aika tare da yunƙurin kisa ne a daƙinsu kwanan ɗalibai mata da ke wajen harabar jami’ar a yankin Malete a ranar 2 ga watan Disamba, 2024.
A yayin gurfanar da matashin a gaban Kotun Majiatare ta Jihar Kwara da ke birnin Ilorin, an tuhume shi da yin amfani da makami wajen yi wa ɗaliban munanan raunuka, tare da yi musu fyaɗe da kuma sace wayoyin iPhone 13 PronMax da iPhone 11 Pro Max.
’Yan sanda na neman ’yan bola-jari ruwa a jallo a Abuja 2027: Kwankwaso da Aregbesola sun gana kan makomar siyasar Najeriya“Kana gab da kashe ɗaya daga cikinsu ne aka kawo musu ɗauki, kuma bincike ya gano cewa kai ɗan ƙungiyar asiri ne tun shekarar 2020, kuma ƙungiyarku ta Aiye, ta yi ƙaurin suna wajen yin fashi da makami da aikata kisa da kuma yi wa ɗalibai mata fyaɗe,” kamar yadda ɗan sanda mai gabatar da ƙara, Nasiru Yusuf, ya karanta a takardar zargin matashin ɗan shekara 26.
Daga nan alƙalin kotun, Majistare Sa’idu ya ba da umarnin tsare wanda ake zargin tare da ɗage shari’ar zuwa ranar 20 ga watan nan na Fabrairu, 2025.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗalibai ɗalibai mata
এছাড়াও পড়ুন:
Za a hukunta ma’auratan da suka ci zarafin yarinya a kan mangwaro — Zulum
Gwamnatin Jihar Borno, ta ɗauki matakin hukunta wasu ma’aurata, Mamman Sheriff da matarsa, da aka kama suna cin zarafin wata yarinya a unguwar Pompomari Bypass da ke Maiduguri.
Bayan bayyanar faifan bidiyon da ya nuna ma’auratan suna dukan yarinyar, mutane da dama sun yi tir da abin a shafukan sada zumunta.
Majalisar Wakilai ta musanta karɓar kuɗi kan dokar ta-ɓaci a Ribas Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar NamibiaWannan ya sa Hukumar Tsaron Sibil Difens (NSCDC) ta cafke su nan take.
Gwamnan jihar, Babagana Umara Zulum, ya tabbatar da cewa gwamnati ba za ta musu sassauci ba.
Ya ce ma’aikatun shari’a, ilimi, da harkokin mata sun haɗa kai domin ganin an hukunta waɗanda suka aikata laifi.
Yarinyar, wacce ɗaliba ce, ta shiga harabar gidan ma’auratan domin tsinkar mangwaro bayan tashi daga makaranta, inda suka yi mata dukan kawo wuƙa.
A halin yanzu tana kwance a asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH), inda Dokta Lawan Bukar Alhaji ya ɗauki nauyin jinyarta.
Gwamnatin Borno ta kuma tallafa wa iyayen yarinyar da kayan agaji, abinci, da kuɗi.
Iyayenta da sauran jama’a sun yaba wa gwamnatin kan matakin da ta ɗauka na kare haƙƙin yarinyar.
Gwamnati ta jaddada cewa duk wanda aka kama da cin zarafin yara ba zai tsira daga hukunci ba.