Netanyahu zai gurfana a kotu kan cin hanci
Published: 10th, February 2025 GMT
Fira Ministan Isra’ila, Banjamin Netanyahu, zai gurfana a kotu kan zargin aikata zamaba da karbar cin hanci da rashawa.
Za a gurfanar da Mista Netanyahu ne daomin ya amsa tambayoyi a shari’ar da aka jima ana zargin sa da aikata manyan laifuka uku na cin hanci da cin amana.
Masu gabatar da kara na zargin sa da aikata laifukan da suka hada da karbar cin hanci da zamba da kuma cin amana.
A kan haka yake fuskantar zargin bayar da cin hanci da kuma cin amanar dukiyar al’umma da aka ba shi.
Ana kuma zargin shi da matarsa da karbar toshiyar baki ta Dalar Amurka 21,000 daga wani furodusa a masana’anatar fina-finan Amurka ta Hollywood, dan kasar Isra’ila mai suna Arnon Milchan, da wani attajirin kasar Australiya, James Packer.
Yana kuma fuskantar zargin kulla yarjejeniyar da mamallakin kamfanin jaridar Yedioh Ahronoth, Arnon Mozes, domin tallata shi, inda shi kuma zai yi dokar da za ta hana bunkasar wata jarida da ke gogayya da Yedioh Ahronoth.
A kan wannan kuma ana zargin Netanyahu da laifin zamba da kuma cin amana.
Tun shekarar 2020 Netanyahu yake fuskantar wadannan zarge-zarge, amma ya musanta aikata ba daidai ba.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Za mu farfaɗo da Madatsar Ruwa ta Biu — Zulum
Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya jaddada kudirin gwamnatinsa na sake farfaɗo da Madatsar Ruwa ta Biu da aka daɗe da watsi da ita domin bunƙasa noman rani da nufin samar da wadataccen abinci a Kudancin Borno da ma Jihar ta Borno gaba ɗaya.
Zulum ya yi wannan alkawarin ne a yayin wata ziyarar ban girma da ya kai wa Mai martaba Sarkin Biu, Mustapha Umar Mustapha, a ziyarar aiki ta kwana uku da ya kai masarautar kwanakin baya.
Wata mata ta haifi jaririn da ba nata ba NAJERIYA A YAU: Yadda watan Ramadana ke tasiri a harkokin kasuwanci“Kokarin farfado da wannan madatsar ruwa na da matuƙar muhimmanci wajen magance ƙalubalen ƙarancin ruwa da aka shafe shekaru biyu ana yi a yankin,” in ji gwamnan.
Ya kuma jaddada cewa, farfado da madatsar ruwan zai dawo da ayyukan noman rani masu yawa a Kogin Hawul, wanda zai amfanar da kananan hukumomi shida na Kudancin Borno.
Da yake jaddada muhimmancin noman rani ga al’umma, gwamnan ya lura cewa, noma ya kasance ginshiƙin manufofin gwamnatinsa, wadda ya ce ita ce manufarsu, domin tabbatar da wadatar abinci da samar da rayuwa mai dorewa, musamman ga wadanda rikicin Boko Haram ya shafa.
Ya kuma tabbatar wa mai martaba sarki da al’ummar Biu cewa, in an kammala madatsar ruwan a 2026 in Allah Ya so, zai kawo sauyi sosai a fannin noma da kuma damar bunkasa tattalin arziki a yankin.
“Aikin noma na daya daga cikin manyan ginshikan gwamnatina, kuma za mu ci gaba da saka hannun jari a fannin don inganta samar da abinci da inganta rayuwar al’ummarmu,” in ji shi.
Gwamna Zulum ya kuma bayyana cewa, za a kara aiwatar da ayyukan raya kasa a masarautar kafin wa’adinsa ya kare a 2027.
Ya kuma jaddada bukatar hadin kan shugabannin siyasa, inda ya bayyana cewa hadin kai zai iya kara habaka tattalin arziki da samar da ababen more rayuwa a fadin jihar.
“Abin farin ciki ne ganin cewa Jihar Borno ba ta fama da rikicin siyasa, ‘yan majalisar dokokinmu na kasa da na jiha da sauran masu rike da mukaman siyasa, sun ci gaba da kasancewa da haɗin kai wajen samar da ribar dimokuraɗiyya,” in ji Zulum.
A nasa martanin, Mai martaba Sarkin Biu Mustapha Umar Mustapha ya yaba wa Gwamna Zulum bisa jajircewarsa wajen gudanar da ayyukan da suka shafi al’umma a Masarautar Biu.
Ya kuma yaba wa gwamnan musamman kan kaddamar da shirin tallafa wa matasa da marasa galihu, wadanda rikicin shekaru 15 na masu ta da kayar baya da aka yi fama da shi a Jihar Borno da ma wasu jihohin makwabta ya shafi rayuwarsu.
Sarkin ya nuna jin dadinsa da tallafin da gwamnatin jihar ke ci gaba da bai wa al’ummar jihar, inda ya tabbatar da cewa, shirin farfado da madatsar ruwa ta Biu da sauran ayyukan raya kasa za su inganta rayuwar mazauna yankin.
Kasancewar noma a sahun gaba a cikin abubuwan da gwamnatinsa ta sa gaba, ana sa ran sake mayar da hankali kan noman rani da Gwamna Zulum ya yi alkawarin zai bunkasa domin inganta tattalin arziki da kuma karfafa juriyar al’ummar Borno kan karancin abinci.