Aminiya:
2025-02-22@06:39:05 GMT

Netanyahu zai gurfana a kotu kan cin hanci

Published: 10th, February 2025 GMT

Fira Ministan Isra’ila, Banjamin Netanyahu, zai gurfana a kotu kan zargin aikata zamaba da karbar cin hanci da rashawa.

Za a gurfanar da Mista Netanyahu ne daomin ya amsa tambayoyi a shari’ar da aka jima ana zargin sa da aikata manyan laifuka uku na cin hanci da cin amana.

Masu gabatar da kara na zargin sa da aikata laifukan da suka hada da karbar cin hanci da zamba da kuma cin amana.

Laifukan sun hada da sa da daga kafar harajin Dala miliyan 500 ga kamfanin sadarwa na Bezeq Telecom domin kamfanin ya tallata shi da matarsa Sara a wani shafin yada labarai. Ɗan fashi ya yi wa ɗaliban jami’a uku fyaɗe ’Yan sanda na neman ’yan bola-jari ruwa a jallo a Abuja

A kan haka yake fuskantar zargin bayar da cin hanci da kuma cin amanar dukiyar al’umma da aka ba shi.

Ana kuma zargin shi da matarsa da karbar toshiyar baki ta Dalar Amurka 21,000 daga wani furodusa a masana’anatar fina-finan Amurka ta Hollywood, dan kasar Isra’ila mai suna Arnon Milchan, da wani attajirin kasar Australiya, James Packer.

Yana kuma fuskantar zargin kulla yarjejeniyar da mamallakin kamfanin jaridar Yedioh Ahronoth, Arnon Mozes, domin tallata shi, inda shi kuma zai yi dokar da za ta hana bunkasar wata jarida da ke gogayya da Yedioh Ahronoth.

A kan wannan kuma ana zargin Netanyahu da laifin zamba da kuma cin amana.

Tun shekarar 2020 Netanyahu yake fuskantar wadannan zarge-zarge, amma ya musanta aikata ba daidai ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Isra ila Netanyahu

এছাড়াও পড়ুন:

USAID: Amurka za ta yi bincike kan ɗaukar nauyin Boko Haram

Gwamnatin Amurka ta ƙudiri aniyar gudanar da bincike kan yadda gwamnatocin da suka gabata suka riƙa sarrafa kuɗaɗen da aka fitar domin bai wa Nijeriya da wasu ƙasashen tallafi.

Hakan dai ya biyo bayan matakin da Shugaban Amurkan, Donald Trump ya ɗauka a watan Janairu na dakatar da duk wani tallafi da Amurkan ke bayarwa a ƙetare har na tsawon kwanaki 90.

DAGA LARABA: Dalilan Da ’Yan Najeriya Ke Haɗa Buga-Buga Da Aikin Albashi Majalisa ta tsayar da ranar sauraron ra’ayin jama’a kan ƙudirin Dokar Haraji

Shugaba Trump ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta gudanar da binciken ne a dalilin ruɗanin da ya dabaibaye duniya wanda ke cin karo da muradun Amurkan.

Haka kuma, Shugaba Trump ya ce za a gudanar da binciken ne domin amsa kiraye-kirayen ke yi wajen bitar ayyukan da Hukumar Bayar da Agaji ta USAID.

A bayan nan ne wani ɗan Majalisar Dokokin Amurka, Scott Perry, ya bayyana cewa hukumar raya kasashe ta Amurka (USAID) ke samar da kuɗaɗe ga kungiyoyin ’yan ta’adda, ciki har da Boko Haram.

Perry ya yi wannan iƙirarin ne yayin zaman sauraron rahoton kwamitin majalisar a kan yadda hukumomin gwamnatin Amurka ke aiwatar da ayyuka da sarrafa kuɗaɗe a ranar Alhamis ta makon jiya.

Zaman mai taken “yaki da barna: Kawar Da Annobar Almundahana Da Zamba,” ya maida hankali ne a kan zargin barnatar da kudaden masu biyan haraji.

“Waye ke samun wani banagare na kudaden? ko wani a ɗakin nan ya kiyaye waɗannan sunaye? saboda kudadenku, dala miliyan 697 a duk shekara, baya ga aika ƙarin kuɗaɗe ga Madrasas da ISIS da Al-Qa’ida da Boko Haram da ISIS Khorasan da sansanonin horas da ‘yan ta’adda. Wadannan su ne abubuwan da take daukar nauyi,” kamar yadda Perry ya bayyana.

Shafin yanar gizon kwamitin ya bayyana cewar zai yi aiki tare da ma’aikatar bin diddigin ayyukan hukumomin gwamnatin Shugaba Trump domin magance barna, da dakile almundahana tare da gudanar da cikakken bincike a kan yadda aka zambaci masu biyan harajin Amurka.

Ƙungiyar Boko Haram, wacce aka sani da Jamā’at Ahl as-Sunnah lid-Da’wah wa’l-Jihād, ƙungiya ce ta ‘yan ta’adda da ta ayyana kanta a matsayin mai tayar da ƙayar baya yankin arewa maso gabashin Nijeriya, da kuma ƙasashen Chadi, Nijar, Kamaru da kuma Mali.

Ƙungiyar ta shafe sama da shekaru 15 tana tashe-tashen hankula a yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya, inda ta kashe dubun-dubatar mutane, a hare-haren da take kai wa ’yan sanda, da sojoji da fararen hula.

Zan gabatar da ƙudiri… — Ndume

A kwanan ne shi ma Sanata Ali Ndume mai wakiltar Borno ta Kudu ya buƙaci gwamnatin Nijeriya ta gaggauta gudanar da bincike kan iƙirarin da ɗan majalisar dokokin Amurka ya yi na cewa hukumar USAID da gwamnatin Trump ta rufe ta tallafa wa ƙungiyoyin ta’addanci da suka haɗa har da Boko Haram a ƙasar.

Ndume ya ce ba batu ba ne da ya kamata gwamnatin Nijeriya ta naɗe hannunta, la’akari da girman barnar Boko Haram a Jihar Borno.

Ya ce zai gabatar da ƙudiri kan binciken zargin ɗan majalisar dokokin na Amurka.

“In an tashi binciken za mu yi tambayoyi, saboda haka za mu bincika domin mu ’yan Nijeriya da abun ya shafa ya kamata mu sa ido don a san matakan da za a ɗauka, saboda ba ƙaramin ɓarna Boko Haram suka yi mana ba,” in ji Ndume.

BBC ya ruwaito Sanata Ndume yana zargin cewa USAID ba ta aiki tare da hukumomin da ya kamata ta yi aiki tare da su a Nijeriya, lamarin da ya ke dasa ayar tambaya.

“Ba sa bari jami’an tsaronmu su sanya ido kan abubuwan da suke yi ballantana su ba da shawara.”

An dai ƙirƙiri Hukumar USAID a shekarun 1960 domin taimaka wa ayyukan agaji a madadin gwamnatin Amurka a kowanne yanki na duniya.

Tana da ma’aikata dubu 10, wanda kashi biyu bisa uku na aiki a ƙetare. Tana da cibiyoyi a sama da ƙasashe 60, sannan tana ayyuka daban-daban a sauran ƙasashe.

Sai dai galibin ayyukanta wasu ƙungiyoyin take bai wa kuɗi su aiwatar, nata shi ne sa ido da tabbatar da cewa an kashe kuɗaɗen bisa tsari.

Ayyukanta na da dimbin yawa. Misali, USAID ba tallafin abinci kaɗai take bayarwa a ƙasashe masu fama da yunwa ba, tana kuma aiki wajen gane inda za a fuskanci fari, da kuma inda za a buƙaci agajin gaggawa na yiwuwar ƙarancin abinci a nan gaba.

Galibin kasafin kuɗin USAID ana kashe su ne a fannin lafiya, irin su rigakafin Polio a ƙasashen da cutar ke yaɗuwa da kuma taimakawa wajen daƙile yaduwar cututtuka da ake yi wa kallon annoba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wasu sassan Abuja za su kasance cikin duhu a ƙarshen mako – TCN
  •  Malaysia: An Bude Kiran Yanke Sayen Kere-kere Kamfanin “Tesla” Na Elon Musk
  • An ƙwace miliyoyin daloli, gidajen da ke da alaƙa da Emefiele
  • Sadaukantaka, Kunya Da Kawar Da Kai Na Annabi Muhammadu (SAW)
  • Amurka Ta Bawa HKI Makami Mai Karfi, MK-87
  • Majalisa ta fara bincike kan zargin USAID na tallafa wa Boko Haram
  • Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba
  • Zargin Daukar Nauyin Boko Haram: Tinubu Na Ganawar Sirri Da Akpabio A Villa
  • Hamas: Za A Mika Gawawwakin ‘Yan Mamaya Da Kuma Fursunoni Rayayyu A Ranakun Alhamis Da Asabar
  • USAID: Amurka za ta yi bincike kan ɗaukar nauyin Boko Haram