Abubuwan da ke faruwa a siyasar jihar a baya-bayan nan sun nuna cewa El-Rufai da Gwamna Sani suna takun saka. A watan Yunin 2024 ne Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta ba da shawarar a binciki El-Rufai kan zargin karkatar da kudaden al’umma.

 

Amma da yake magana a yayin tattaunawar, Bello ya ce, “Babu daya daga cikinsu (Sani da El-Rufai) da ya ba ni labarin rikicin; amma na fahimci cewa, komai ya wuce.

 

Da aka tambaye shi ko zai iya sasanta mahaifinsa da Sani, Bello ya ce, “Ba aikina ba ne. Aikina shi ne in mayar da hankali wajen taimaka wa al’ummar mazabar Kaduna ta Arewa.”

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Iran Ta Jaddada Aniyarta Ta Daukan Fansa Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila

Kwamandan dakarun juyin juya halin Musulunci na rundunar sararin samaniya ya jaddada cewa; Babu shakka Iran zata kaddamar da harin daukan fansa kan haramtacciyar kasar Isra’ila na alkawarin gaskiya na 3

Kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na rundunar Sojin sararin samaniyar Iran, Birgediya Janar Amir Ali Hajizadeh, ya jaddada cewa za a gudanar da farmakin daukan fansa na Alkawarin Gaskiya na 3 idan Allah Ya yarda, amma Iran ba zata barnatar da kwarewarta a banza  kamar yadda ya faru a harin alkawarin Gaskiya ta 1 da ta 2 ba, don haka babu shakka za a gudanar da harin daukan fansa kan haramtacciyar kasar Isra’ila.

Ya kara da cewa: Yankin yammacin Asiya ya samu ci gaba da dama, kuma wannan yanki shi ne tushen al’amuran duniya da dama, to amma a baya-bayan nan ya fara ne da harin daukan fansa na Ambaliyar Al-Aqsah  wanda kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta tsara ta kuma aiwatar da shi, wanda ya zama babbar nasara a kan ‘yan sahayoniya, wannan lamari ne mai muhimmanci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sanata Katung ya damu kan yadda wasu ke ta’azzara ta’addanci a kudancin Kaduna
  • Sanata Katung ya damu kan yadda wasu ta’azzara ta’addanci a kudancin Kaduna
  • Babban mai kai wa Bello Turji makamai ya shiga hannu
  • Abiola Ne Ya Lashe Zaɓen Shugaban Ƙasa Na 12 Ga Watan Yuni 1993 – Janar IBB
  • Jami’an tsaron al’umma 6 sun mutu a artabu da ’yan bindiga a Sakkwato
  • Jami’in tsaron al’umma 6 sun mutu a artabu da ’yan bindiga a Sakkwato
  • Gidauniyar Tunawa Da Sir Ahmadu Bello Za Ta Gudanar Da Taronta Karo Na 11 A Bauchi.
  • Kasar Iran Ta Jaddada Aniyarta Ta Daukan Fansa Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Ukraine ce mai laifi a yaƙin da ta ke yi da Rasha — Trump
  • An Rantsar Da Sabbin Shugabannin Kungiyar Manyan Sakatarorin Jihar Zamfara