HausaTv:
2025-02-21@14:36:20 GMT

Masar Za Ta Karbi Bakuncin Taron Gaggawa Na Larabawa Kan Batun Falasdinu

Published: 10th, February 2025 GMT

Ma’aikatar harkokin wajen Masar ta sanar cewa, kasar za ta karbi bakuncin taron gaggawa na kasashen Larabawa a ranar 27 ga watan Fabrairun nan, domin tunkarar al’amura na baya-bayan nan da suka shafi batun Falasdinu da zirin Gaza.

Sanarwar ta ce, an yanke shawarar gudanar da taron ne bayan muhimman shawarwarin da Masar ta yi da kasashen Larabawa, ciki har da Falasdinu da ta bukaci gudanar da taron, tare da hadin gwiwar Bahrain.

A wani labarin kuma, kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC ta yi kakkausar suka kan munanan kalamai da kuma rashin da’a da firaministan Isra’ila ya yi na yin kira da a kafa kasar Falasdinu a kasar Saudiyya.

A ranar Alhamis, ne Netanyahu ya ba da shawara yayin wata hira da tashar 14 ta Isra’ila cewa “Saudiyya za ta iya kafa kasar Falasdinu a Saudiyya, suna da kasa mai girma.”

Kungiyar ta OIC ta dauki wannan a matsayin tsokana ga Saudiyya, kuma cin zarafi ne ga ’yancin kai, tsaron kasa da kuma yankinta, da kuma keta dokokin kasa da kasa da kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya.

A yayin wani taron manema labarai na hadin gwiwa a birnin Washington da firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ne a ranar Talata, shugaban Amurka Donald Trump ya ce Amurka na shirin “karbe ikon zirin Gaza,” da tura Falasdinawa zuwa kasashe makwabta, da kuma sake raya yankunan gabar tekun,  kalaman na Trump da Netanyahu sun haifar da cece-kuce a yankin da ma duniya baki daya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministoci Za Su Fara Gabatar Da Rahoton Ayyuka A Taron Manema Labarai  

Ta ƙara da cewa wannan shiri yana nuna jajircewar gwamnati wajen tabbatar da gaskiya, riƙon amana, da hulɗa kai-tsaye da jama’a.

 

Za a fara jerin tarukan ne da gabatarwar Ministan Raya Kiwo, Mukhtar Maiha; da Ministan Cigaban Yankuna, Injiniya Abubakar Momoh.

 

Ma’aikatar ta gayyaci ‘yan jarida, masu ruwa da tsaki, da jama’a gaba ɗaya don halartar wannan muhimmiyar tattaunawa da nufin bayyana wa jama’a irin cigaban da gwamnati ke samu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An tara Naira 16 a taron ƙaddamar da littafin IBB
  • Jami’an Diblomasiyya Daga Kungiyar G20 Da Dama Sun Isa Afrika Ta Kudu
  • Ministoci Za Su Fara Gabatar Da Rahoton Ayyuka A Taron Manema Labarai  
  • Dakarun Kai Daukin Gaggawa Sun Kashe Mutane Fiye Da 400 A Yankin Al-Qatana Da Ke Jihar White Nile Ta Sudan
  • Nijar: Taron Kasa Ya Bukaci Sojoji Su Yi Mulkin Rikon Kwarya na Shekara 5
  • Saudiyya ta Gayyaci Kasashen Larabawa Kan Batun Kan Batun Gaza
  • Turkiya Ta Karbi Bakuncin Tattaunawar Sulhu Tsakanin Habasha Da Somaliya
  • Kungiyoyin Falasdinawa A Gaza Sun Bukaci Yin Taron Musamman Domin Dakile Batun Tilasa Wa Mutanen Gaza Yin Hijira
  • Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Da Sarkin Kasar Qatar Kan Muhimmancin Hadin Gwiwa Da Taimakekkeniya Tsakaninsu
  • Sojojin Sudan Sun Killace Fadar Shugaban Kasa Da Take A Hannun ‘Yan Tawayen A Birnin Khartum